’Yan sanda sun ba al’ummar Sheka awa 24 su kawo sunayen ’yan daba
Published: 10th, February 2025 GMT
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano ya ba al’ummar yankin Sheka awa 24 su kawo wa rundunar sunayen manyan ’yan daban da ke addabar yankin.
Rundunar ta ba da wannan wa’adin ne bayan matsalar ’yan daba ta ya ƙi ci ta ƙi cinyewa a yankin da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso.
A yayin wani zama na musamman da kwamishinan rundunar ta yi da al’ummar yankin ne aka ba su wannan sanarwar.
Kwamishinan ’yan sandan, wanda ya samu wakilci DPO na yankin Dakata, ACP Yusha’u Mus’ud, ya ce muddin al’umma ba su taimaka da bayanan jagororin ’yan daban ba, ta ɓata-garin an kama su ba, babu yadda za a yi ɓata-garin su daina addabar yankin.
Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe NAJERIYA A YAU: Shin Har Yanzu Akwai Masu Rufin Asiri A Najeriya?উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan daba bata gari
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya ya kada kuri’ar nuna goyan baya ga wani kudiri da ya jaddada cewa shirin da Morocco ta gabatar kan Yammacin Sahara shi ne mafita ‘’mafi dacewa” ga yankin da ake takaddama a kai.
Kudirin ya nuna goyan bayan kasashe mambobin kwammitin ga shirin na Morocco, tare da bayyana cewa ikon masarautar kan yankin zai iya kasancewa mafita mafi dacewa.
Kan hakan ne kwamitin yaya kira ga Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya António Guterres da wakilinsa na musamman kan wannan batu, Staffan de Mistura, da su gudanar da tattaunawa “bisa ga” wannan shirin don cimma yarjejeniya da kowa zai aminta da ita.
Aljeriya wacce ta ke kaddama da Morocco kan yankin ta kaurace kada kuri’an kan batun inda ta bayyana matukar adawarta da kudirin.
Jakadan Aljeriya, Amar Benjama, ya ce kudirin bai dace da burin mutanen Yammacin Sahara, wadanda kungiyar Polisario ke wakilta ba.
Kudurin da aka amince da shi a ranar Juma’a ya kuma tsawaita aikin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya a Yammacin Sahara (MINURSO) na tsawon shekara guda.
Shirin wanda Rabat ta gabatar a ranar 11 ga Afrilu, 2007, don mayar da martani ga kiran da Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya yi na samar da mafita ta siyasa game da yankin na yammacin Sahara.
Kudirin na yanzu ya tanadi samar da gwamnati da shugaban yankin, da majalisar dokoki wadda ta kunshi wakilan kabilun Sahrawi daban-daban da membobi da aka zaba ta hanyar zaben gama gari kai tsaye.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci