2025-11-10@23:10:04 GMT
إجمالي نتائج البحث: 2663
«Hajiya Sutura»:
(اخبار جدید در صفحه یک)
Sakataren Majalisar Tsaron Kasa ta Iran Ali Larijani (SNSC) ya ce dangantakar da ke tsakanin Tehran da Islamabad tana habaka, kuma za ta iya kaiwa matsayin babban hadin gwiwa na din-din-din. Ali Larijani, a yayin da yake yin wata ganawa da Ministan Harkokin Cikin Gida na Pakistan Syed Mohsin Naqvi a wannan Talata a birnin Tehran, ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar ƙasashen biyu a fannin tattalin arziki. Ya nuna yarjejeniyar dabarun da aka cimma a cikin kwanakin nan tsakanin Pakistan da Saudiyya, a matsayin mataki mai kyau kuma na hikima, wanda yake da tasiri matuka ga irin barazana da kasashen musulmi sue fuskata daga makiya. Larijani ya ce yanayin yankin a yau yana cike da ƙalubale daga maƙiya, wanda ke...
Firayim Ministan Iraki Mohammed Shia al-Sudani ya jaddada cewa wajibi ne a kan al’ummar Iraki kare ‘yancin kundin tsarin mulkin kasarsu wanda hakan ba zai yiwuwa ba sai hanyar tsara makomar kasar ta hanyar sahihin zaben ‘yan majalisar dokoki da ke tafe. Al-Sudani ya jaddada cewa babu wani uzuri na kin kauracewa zabe da za a yarda da shi, yana mai bayyana cewa yin hakan “zai share fagen dawowar wadanda suka gaza da kuma wadanda suka ci hanci da rashawa.” Ya ce, “Muna dogaro da shiga cikin harkokin zabe cikin sani da himma a ranar 11 ga Nuwamba, ranar da za mu tsara sabuwar makomar siyasa ta Iraki.” Ya fayyace, “Muna son manufofin hikima da fifita muradun Iraki da al’ummar...
Sama da Falasdinawa 60, ciki har da yara 22 ne suka yi shahada a jerin hare-haren jiragen yakin Isra’ila suka kai a wurare da dama a yankin Gaza A cikin sa’oin da suka gabata, A cewar majiyoyin lafiya. Jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare a lokaci guda kan gidaje, masallatai, da sansanonin ‘yan gudun hijira. Wakilin Al-Mayadeen ya ruwaito cewa an kai wani harin bam a kan gidan iyalan Abu Dalal da ke sansanin ‘yan gudun hijira na Nuseirat, inda aka kashe mutane 10, ciki har da yara uku. An kuma kai hari gidan iyalan Aql da ke sansanin, wanda ya yi sanadiyyar shahadar mutane uku da kuma jikkata da dama, yayin da Isra’ila take ci gaba da kai hari...
Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya umarci rundunar sojin ƙasar da ta kai mummunan farmaki a Zirin Gaza, bayan ya zargi ƙungiyar Hamas da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma. Wata sanarwa da ofishin firaministan ya fitar, ta ce: “Bayan tattaunawar tsaro, Firaminista Netanyahu ya umurci rundunar soji da ta gaggauta kai hare-hare masu ƙarfi a Zirin Gaza.” Juventus ta kori kocinta Igor Tudor An raba wa iyalan ’yan sandan da suka mutu tallafin N31m a Jigawa Sanarwar na zuwa ne bayan Isra’ila ta zargi Hamas ta karya sharuɗɗan yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma kwanakin baya domin ba da damar kai agaji ga fararen hula da ke yankin. Tun da farko dai Netanyahu ya sha alwashin mayar da martani...
“Bayan gano alamun karkatar da kudaden tallafin a matakin farko, mun gabatar da matakai don tabbatar da cewa kudin ya isa ga wadanda aka yi niyya,” in ji shi. Wasu daga cikin matakan da aka dauka sun hada da kafa kwamitin mambobi 20 a kowace karamar hukuma, wanda ya kunshi sarakunan gargajiya, shugaban karamar hukuma, shugaban jam’iyya, da sauran mambobi. Ya yi kira ga wadanda suka amfana da tallafin da su yi amfani da kudaden ta hanyar kafa kananan kasuwancin kashin kansu domin inganta yanayin samun kudinsu da zamantakewarsu domin habaka tattalin arzikinsu da kuma na iyalansu. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba October 28,...
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta bayyana cewa duk da jajircewar kungiyar na mutunta yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma da ita, firaministan gwamnatin Isra’ila yana kokarin karya sharuddanta. Hazem Qassem, kakakin kungiyar, ya ce “Mun yi wa masu shiga tsakani bayani kan cikas din da ke hana neman gawarwakin fursunonin Isra’ila kuma mun nemi su samar mana da karin kayan aiki.” Mai magana da yawun Hamas ya kuma bayyana cewa: “Mun sanar da Alkahira game da ayyukan bincike na ‘yan Isra’ila, kuma muna ci gaba da sanar da masu shiga tsakani game da ci gaban binciken. Duk da tsagaita wuta da aka yi tsakanin gwamnatin Tel Aviv da kungiyar Hamas, sojojin Isra’ila sun ci gaba da kai hare-hare. Na...
Jakadan China a Iran ya ce kasarsa za ta dauki mataki idan takunkumin da aka sanya wa Iran ya shafi muradun ta. A wani taron manema labarai da aka gudanar a Tehran jami’in diflomasiyyar naChina ya ce Beijing “ba za ta yi jinkirin daukar mataki ba” idan sabbin takunkumin suka shafi cinikayyarta da Iran. Wadannan kalamai sun zo ne a matsayin martani ga tambayoyi game da matsayin China kan takunkumin Majalisar Dinkin Duniya da aka sake kakaba wa Iran, wanda aka sake kakabawa a karshen watan Satumba bayan da kasashen Turai da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar nukiliya ta 2015 suka zargi Tehran da gaza cika wajibcin da ke kanta a karkashin yarjejeniyar. Jakadan Chinar ya kuma nuna cewa Beijing...
Rundunar ’yan sandan Jigawa ta raba tallafin Naira miliyan 31 ga iyalan jami’ai 59 da suka rasa rayukansu a bakin aiki. Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, inda ya bayyana cewa wannan mataki na nuna irin ɗawainiyar da rundunar ‘yan sandan ke yi wajen kula da jin daɗin jami’anta da iyalansu. Majalisar Dattawa za ta tantance sabbin hafsoshin tsaro ranar Laraba Rikicin adawa da cin zaben Shugaba Paul Biya ya bazu a Kamaru Aminiya ta ruwaito cewa Kwamishinan ‘yan sandan Jigawa, CP Dahiru Muhammad ne ya wakilci Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Adeolu Egbetokun, wajen raba tallafin a ƙarƙashin shirin nan na tallafa wa iyalan...
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Haɗin kai a tsakanin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya ba zaɓi ba ne, amma dole ne Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Hadin kai da hadin gwiwar kasashen yankin Gabas ta Tsakiya a cikin tsarin Kungiyar Hadin Kan Tattalin Arziki (ECO) ba wani zaɓi ne na siyasa ba, a’a, wani muhimmin abu ne don cimma ci gaba, tsaro, da kwanciyar hankali a yankin. A lokacin jawabinsa a taron Ministocin harkokin cikin gida na kasashe membobin ECO na hudu, Pezeshkian ya lura cewa: Kiran wannan taron bayan dogon hutu yana nuna sha’awar kasashen membobinta na inganta hadin kai da hadin gwiwa a muhimman fannoni da ke shafar dangantakar yankuna. Ya bayyana cewa ma’aikatun...
Mataimakin Ministan Harkokin Waje Kan Harkokin Siyasa Na Iran Ya Ce: Iran Ba Ta Kula Da Matsin Lamba
Mataimakin Ministan Harkokin Waje kan Harkokin Siyasa na Iran ya bayyana cewa: Iran ta yi imani da diflomasiyya amma ta yi watsi da duk wata tattaunawar dole da aka tilasta mata Mataimakin Ministan Harkokin Waje na Harkokin Siyasa na Iran ya jaddada cewa: Iran ta yi imani da diflomasiyya, amma ta yi watsi da duk wata tattaunawa da aka tilasta mata bin duk wani ra’ayin wani bangare guda. Ya jaddada cewa: Warware takaddama cikin lumana zai yiwu ne kawai idan bangarorin biyu suna kan daidaito kuma babu wanda ke neman sanya sharuddansa. A lokacin taron kasa da kasa na hudu na nazarin Iran na zamani, a wani zama mai taken “Iran da Duniya Bayan Yakin Kwanaki 12,” Mataimakin Ministan Harkokin...
Iran, a matsayinta na ƙasa mai wayewa da wayewa, ta kasance mai himma wajen haɓaka zaman lafiya da tsaro a duniya, in ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Waje Esmail Baqaei a ranar Litinin a gefen wani biki na cika shekaru 80 da kafa Majalisar Dinkin Duniya a Tehran. A cewar Pars Today, Baqaei ya ƙara da cewa a cikin ‘yan shekarun nan, an sami manyan keta ƙa’idodi da manufofin Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya, waɗanda suka yaɗu a duk duniya. Ya yi gargaɗin cewa rashin kula da manufofin Majalisar Dinkin Duniya ya sanya zaman lafiya da tsaro a duniya cikin haɗari mai girma. Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya jaddada cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sake jaddada buƙatar...
Mai bai wa jagoran juyin musulunci na Iran shawara akan harkokin siyasar kasa da kasa Dr. Ali Akbar Wilayati ya ce; Da akwai kasashe uku a cikin Asiya wadanda suke da ‘yanci da su ne Iran, China da Rasha, kuma suna taka rawa domin samar da sabon tsarin tafiyar da duniya. Dr. Wilayati ya bayyana hakan ne dai a yayin ganawarsa da jakadan China a Iran “Zong Bi Wuu” yana mai kara da cewa; Alaka a tsakanin kasashen biyu ta dade da kuma zurfi. Har ila yau Wilayati ya ce alakar kasashen biyu ta ginu ne akan maslaha da kuma girmama juna da kuma cin gashin kai na siyasa, da hakan ya mayar da su, tare da kasar Rasha zama...
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce hadin kai tsakanin kasashen Musulmi yana da matukar muhimmanci wajen kare muradunsu da tsaronsu, daga duk wani cin zarafi daga kasashen waje. Mista Pezeshkian ya yi wannan furuci ne a wata ganawa da Ministan Harkokin Cikin Gida na Oman Sayyid Hamoud bin Faisal al-Busaidi a Tehran yau Litinin. Da yake nuni da kyakkyawar alakar da ke tsakanin Iran da Oman, wacce ya ce ta kasance bisa girmama juna da kuma kyautatawa. Shugaban ya ce kasashen biyu ko yaushe suna goyon bayan junansu ta hanyar ci gaban yankin. Ya yaba da rawar da Oman ta taka a ci gaban yankin, musamman a fannin sulhu da kuma karbar bakuncin tattaunawa tsakanin Iran da Amurka. Iran...
Jamhuriyar Musulinci ta Iran, ta bukaci Majalisar Dinkin Duniya da ta nisanci nuna bangaranci a cikin ayyukanta musamman game da yadda Amurka da Isra’ila ke keta dokokin kasa da kasa. Da yake bayyana hakan mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmail Baghai ya yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya da ta zama wakiliya game da hakkokin duk kasashe, yayin da yake yabon ka’idojin kungiyar. Ya bayyana hakan ne a lokacin da MDD ta cika shekaru 80 da kafuwarta. Mista Baghai Ya Yi Allah wadai Da ta’addancin Da Amurka Da Isra’ila Suka Yi Wa Iran A Watan Yunin Da Ya Gabata. Iran ma ta bi sahun wasu kasashe a duniya da a ranar Litinin din nan, 27 Ga...
Shugaban majalisar Mohammad Baqer Qalibaf ya bayyana cewa, wasika ta hadin gwiwa da Iran, Rasha da China suka aike wa Majalisar Dinkin Duniya a cikin ‘yan kwanakin nan, da ke adawa da yunkurin Turai na sake dawo da takunkumi kan Iran wannan ya nuna hadin gwiwa mai karfi a tsakanin manyan kasashen uku. Ya yi wannan jawabin ne a lokacin wani zaman majalisa a Tehran a ranar Lahadi, mako guda bayan da kasashen uku suka mika wa babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da shugaban Kwamitin Tsaro wasikarsu, inda suka tabbatar da kawo karshen aikin kuduri mai lamba 2231, wanda ya amince da yarjejeniyar nukiliya ta 2015 wadda Amurka ta yi watsi da ita. “A cikin ‘yan kwanakin nan, mun shaida...
Sakataren Hezbollah, Sheikh Naim Qassem, ya tabbatar da cewa Hizbullah ta shirya don fuskantar isra’ila, yana mai bayyana cewa duk da cewa ba su da niyar fara yaki, amma suna shirye su kare Lebanon idan yaki ya barke. Sheikh Qassem a zantawarsa da tashar Al-Manar TV ya jaddada cewa idan aka tilasta musu yin yaki, tabbas za su fuskanci Isra’ilawa da dukkanin karfinsu, kuma ba za su bar Isra’ila ta mamaye kudancin Lebanon ba,ko da kuwa hakan zai kai ga shahadarsu ne baki daya. Ya yi ishara da irin ayyukan wuce gona da iri da isr’ila ke yi akullum rana ta allaha kan kasar Lebanon a kan idanun duniya, wanda hakan ya yi hannun riga da yarjejeniyar dakatar dayaki da...
Wani ɗalibin Jami’ar Jos da ke Jihar Filato, ya kashe abokinsa, wanda shi ma ɗalibi ne a jami’ar, sannan ya binne gawarsa a bayan gidansu. Wanda aka kashe mai suna Peter Mafuyai, ɗalibi ne da ke shekara ta uku a sashen hada-hadar kuɗaɗen banki. Dangote na shirin faɗaɗa matatarsa don zama mafi girma a duniya Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — Dasuki Ana zargin Nanpon Timnan da ke ajin shekara ta biyu daga sashen karatun harkar noma, da kashe shi sannan ya binne shi a rami. Rahotanni sun bayyana cewar ɗaliban abokan juna ne sosai. An ruwaito sun fita ƙwallon ƙafa, daga nan suka wuce wani waje sannan suka dawo gida. “Da suka dawo...
Wani ɗalibin Jami’ar Jos da ke Jihar Filato, ya kashe abokinsa, wanda shi ma ɗalibi ne a jami’ar, sannan ya binne gawarsa a bayan gidansu. Wanda aka kashe mai suna Peter Mafuyai, ɗalibi ne da ke shekara ta uku a sashen hada-hadar kuɗaɗen banki. Dangote na shirin faɗaɗa matatarsa don zama mafi girma a duniya Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — Dasuki Ana zargin Nanpon Timnan da ke ajin shekara ta biyu daga sashen karatun harkar noma, da kashe shi sannan ya binne shi a rami. Rahotanni sun bayyana cewar ɗaliban abokan juna ne sosai. An ruwaito sun fita ƙwallon ƙafa, daga nan suka wuce wani waje sannan suka dawo gida. “Da suka dawo...
Kungiyar gwagwamaryar Falasdinawa ta Hamas ta bayyana cewa ba za ta bari Isra’ila ta samu wata hujja ta ci gaba da yaki a Gaza ba. Khalil al-Hayyah jigo a kungiyar ta Hamas, ya nuna gazawar gwamnatin Isra’ila na cimma burinta a Gaza kuma ya bayyana cewa kungiyar tana mutunta dukkan alkawuran da ta dauka a karkashin yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma ba kuma ba za ta bari makiya su sami hujjar ci gaba da yakin ba. al-Hayyah, shugaban ofishin siyasa na Hamas a Gaza, ya bayyana a wata hira da tashar Al Jazeera cewa gwamnatin Isra’ila ta gaza cimma duk wani burinta a lokacin yakin kuma Hamas za ta yi duk mai yiwuwa don hana sake barkewar yaki. Da...
Mataimakin shugaban ƙasar ya ƙara da cewa kwamitin shugaban ƙasa kan ba da tallafi ya ƙaddamar da rabon naira miliyan 50, inda mutum miliyan 1 za su samu naira dubu hamsin kowanensu tare da wasu shirye-shirye na bunƙasa ƙananan sana’o’i. Ya ƙara da cewa ƙanana da matsaƙaitan sana’o’i a Jihar Katsina za su samu 250,000 daga gwamnatin tarayya wanda zai taimaka wa sana’o’insu wajen bunƙasa tattalin arzikin Nijeriya Da yake jawabi a wajen taron, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa ya bayyana cewa gwamnatinsa tana aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatin tarayya wajen ƙirƙirar ayyuka, wanda yanzu haka an samar da kuɗaɗai har naira biliyan 5.5, inda aka raba biliyan ɗaya ga mutane 701 a faɗin jihar. Gwamna Raɗɗa...
Dasuki, wanda shine shugaban rikon kwarya na Shirin Makomar Matasa A Yanzu, wani shiri na hada matasa da harkokin siyasa da aka kaddamar a ranar 1 ga Oktoba, 2025 a Abuja, ya bayyana cewa sanarwar shirin na cewar kashi 70% na kujerun majalisar wakilai a zaben 2027 su kasance na ‘yan Nijeriya kasa da shekaru 40, ba kawai magana ce ta fafutuka ba, har ila yau kalubale ne ga shugabanni. Matakin Dasuki ya kasance wani muhimmin lamari a farfajiyar siyasar Najeriya, inda ’yan siyasa kalilan ke ja da baya daga mukaman su. Sanarwar sa an fassara ta sosai a matsayin wakilcin gwagwarmayar adalci tsakanin tsararraki wanda ya taimaka wajen jagoranta, wanda ke nufin rage gibin da ke tsakanin tsofaffi...
Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci ya fadawa shugaban Amurka Trump cewa ya ci gaba da rayuwar cikin mafarkinsa! A jawabin da ya gabatar a gaban Majalisar Dokokin Isra’ila ta “Knesset”, Shugaban Amurka Donald Trump ya yi ikirarin cewa ya lalata cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya, amma kalmomi biyu kacal da Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci a Iran, Ayatollah Sayyed Ali Khamenei, ya furta sun isa su zame a matsayinsa mayar da martani. Ya zo cikin Shafin Jagoran juyin juya halin Musulunci cewa: Alfaharin Shugaban Amurka cewa: “Hakika sun yi luguden wuta kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran tare da ruguza su, tabbas wannan da’awa ce kawai, amma Amurkawa su ci gaba da rayuwa cikin wannan ruɗunsu!” Martani mai ƙarfi...
Wani rahoto na kafar watsa labarun Birtaniya ya bayyana cewa; Da akwai fiye da fursunoni 90 da suke yajin cin abinci a gidan kurkukun kasar Bahrain suna neman a sake su. Rahoton ya kuma ce, mafi yawancin fursunonin da suke yajin cin abincin suna babban gidan yarin kasar ne, kuma an kama su da yi musu hukunci ne bisa dalilai na siyasa. Wannan dai ba shi ne karon farko ba da fursunoni a kasar Bahrain suke yajin cin abinci bisa nema a kyautata yanayin rayuwarsu a inda ake tsare da su, ko kuma neman a sake su ba tare da wani sharadi ba. Wani sauti na daya daga cikin fursunonin da aka dano daga cikin gidan kurkuku, ya bayyana cewa;...
Babban sakataren Majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani ya bayyana cewa; Bayan da aka dauki shekaru biyu ana yi wa mutanen Gaza kisan kiyashi, wanda mutane 70,000 su ka yi shahada, wasu fiye da 100,000 su ka jikkata, suna son a rufe wannan laifin da taron zaman lafiya. Ali Larijani ya kara da cewa; Sun kashe al’ummar Falasdinu, sun hana shi abinci da ruwa, yanzu kuma suna son bayyana kawukansu a matsayin masu ceto da Falasdinawa, don haka wannan taron ba komai ba ne sai wasan kwaikwaiyo. Taron da aka yi a Sherm-Sheikh na Masar an yi shi ne a karkashin jagorancin shugaban Amurka Donald Trump wanda kasarsa ce ta kasance a gaba wajen bayar da makamai ga...
Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU, ta ƙaryata labaran da ke yawo a kafafen sada zumunta, cewa tana aikin ƙera makamin nukiliya a ɓoye a cikin jami’ar. A wata sanarwa da ofishin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na jami’ar, ƙarƙashin Malam Auwalu Umar, ya fitar, jami’ar ta bayyana cewa labaran da ake yaɗawa ba su da tushe balle makama. Boko Haram na amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare — Zulum ’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam “Mun lura da wani faifan bidiyo da na’urar AI ta ƙirƙira, wanda wasu ke yaɗawa suna iƙirarin cewa ABU na ƙera makamin nukiliya a ɓoye. Wannan ƙarya ce babu gaskiya a cikinta,” in ji...
Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zaria, ta karyata wani faifan bidiyo da aka yada a kafafen sada zumunta da ke zargin cewa jami’ar na da hannu wajen wani shiri na sirri kan hada makamin nukiliya a Nijeriya. A wata sanarwa da Daraktan hulda da jama’a na jami’ar, Malam Auwalu Umar, ya fitar a ranar Asabar, jami’ar ta bayyana cewa wannan faifan bidiyon da aka samar ta hanyar na’urar kirkirar bidiyo, karya ne kuma an shirya shi ne don rikita jama’a da bata hakikanin manufar kasar wajen amfani da makamashin nukiliya. Umar ya jaddada cewa dukkan aiyukan nukiliyar Nijeriya ana gudanar da su ne bisa tsarin lumana da kuma bin ka’idodin kasa da kasa kamar yarjejeniyar NPT da Pelindaba Treaty, wadda ta...
Ta hanyar aikinsa, Adeyemi yana nuna cewa ƙirƙira tana da ƙarfi sosai lokacin da take bauta wa bil’adama. Manhajarsa, wacce yanzu ake gwadawa a makiɗa da dama na manyan makarantu, ba kawai tana ba da damar samun ilimi bace, har ma da haɗa ɗalibai cikin zamantakewa, tana taimaka wa aiki ga ɗalibai masu rauni a gani bane kawai, su yi hulɗa da ƙwarin gwiwa a cikin ajujuwa da muhallin dijital. A wannan ma’anar, gudummawarsa ta kasance fasaha da ɗan’Adam: tana cike giɓi, faɗaɗa dama, kuma tana ƙalubalantar tunanin da aka saba game da naƙasa da ƙwarewa. Tafiyar Adeyemi tana nuna haɗin kai tsakanin ƙwarewar fasaha da shugabanci mai manufa. Bayan ya yi horo a Kimiyyar Kwamfuta a Coɓenant Uniɓersity, ya...
Ya ƙara da cewa cibiyar Centre for Energy Research and Training (CERT) ta jami’ar ABU, wadda aka kafa tun 1976, tana aiki tare da IAEA da kuma ƙasashe kamar Amurka, da Rasha da China, kuma ba ta taɓa gudanar da wani shiri na makamin nukiliya ba. A cewarsa, “ABU tana ci gaba da sadaukar da kai wajen inganta kimiyya da fasaha don ci gaban ƙasa da kuma tabbatar da zaman lafiya ta hanyar amfani da makamashin nukiliya ta hanya mai amfani da jama’a.” ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu October 25, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi October 25, 2025 ...
Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Kiran Da A Nisanci Siyasantar Da Kwamitin Tsaron Majalisar
Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa: Bai kamata a yi mummunan amfani da kwamitin tsaron ba ko kuma a yi amfani da shi don dalilai na siyasa Jakadan Iran kuma wakilin dindindin a Majalisar Dinkin Duniya Amir Sa’ed Irawani, ya bayyana cewa: An gwada Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya sosai ta hanyar ayyukan ta’addanci da kuma amfani da dabarunta na siyasa. Ya ce: “Dole ne kwamitin tsaro ya cika nauyin da ke kansa da mutunci, inganci, kuma ba tare da son kai ba. Babu wani memba, komai karfi da zai iya amfani da wannan cibiyar ba bisa ka’ida ba ko kuma ya yi amfani da shi don dalilai na siyasa ko na bangare guda.” A jawabinsa a Majalisar...
Tsohon Shugaban Hukumar Leken Asirin Dakarun IRGC Ya Ce: Yakin Kwanaki 12 Kan Iran Ya Canza Tunanin Makiya
Tsohon shugaban hukumar leƙen asiri ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Yaƙin da aka ɗora wa Iran ya canza daidaiton da ke tsakanin Sahayonayya da Amurka Tsohon shugaban hukumar leƙen asiri ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC), Hussein Ta’ib, ya ce: Yaƙin kwanaki 12 da gwamnatin sahayoniyya ta ɗora wa Iran, ba wai kawai bai cimma komai ga Isra’ila ba ne, har ma ya canza daidaiton dabarun Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila gaba ɗaya. A lokacin taron tattaunawa na 31 na ƙungiyar Jaruman Musulunci a Qom, Hussein Ta’ib ya ce: “Dakarun kare juyin juya halin Musulunci da sojojin Iran sun kalubalanci masu girman kai inda suka kai wani mataki cikin saurin na zarce lissafin...
Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Gombe, Kanal Abdullahi Bello (mai ritaya), ya rasu a hatsarin mota. Gwamnatin Jihar Gombe ce, ta sanar da rasuwar cikin wata sanarwa da Daraktan Harkokin Watsa Labarai, Ismaila Uba Misilli, ya fitar a ranar Juma’a. Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC Gwamnan Bauchi ya naɗa ɗan uwansa a matsayin sabon Sarkin Duguri Sanarwar ta ruwaito cewa Bello ya rasu a kan hanyar Malam Sidi zuwa Gombe, bayan aukuwar wani mummunan hatsarin mota. “Gwamnatin Jihar Gombe na cikin jimamin sanar da rasuwar Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Kanal Abdullahi Bello (mai ritaya), sakamakon a hatsarin mota da ya rutsa da shi a kan hanyar Malam Sidi...
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da Majalisar Abinci Mai Gina Jiki ta Jihar Jigawa 774, inda ya tabbatar da kudurin gwamnatinsa na yaki da rashin abinci mai gina jiki da inganta yalwar abinci a fadin jihar. An gudanar da kaddamarwar ne yayin ziyarar Mrs. Uju Rochas-Anwuka, mai bai wa Shugaban Kasa shawara ta musamman kan lafiya ( Karkashin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa), wacce ta je Jigawa domin kaddamar da shirin Nutrition 774 da ke karkashin shirin sabunta kudurori na Renewed Hope Agenda. Gwamna Namadi ya bayyana cewa Jigawa ta kasance gaba a yaki da matsalar, tare da kafa shiri na musamman da aka yi wa lakabi da Masaki tun a 2020 domin fadakar da al’umma a...
‘Yan sandan kasar Ghana sun sanar da cewa tserato da wasu ‘yan Najeriya 57 da aka yi faskwaurinsu, haka nan kuma wasu mutane 5 da suke aikata laifuka ta hanyar sadarwar na “Internet” Jami’an ‘yan sandan sun kwace nau’ra mai kwakwalwa 77 da wayoyin hannu 38, sai kuma wasu motoci 2, akwatin talbijin 3, da kuma wasu na’urori da suke amfani da su a yaudarar mutane. A ranar Larabar da ta gabata ne jami’an ‘yan sandan kasar ta Ghana su ka sanar da kai farmakin a birnin Accra a ranar Laraba 22 ga watan nan na Oktoba. Shekarun mutanen da ake amfani da su wajen yaudarar mutane ta hanyar internet suna a tsakanin 18 zuwa 26,tuni kuma an kai su...
Kungiyar ‘yan wasan kokawar Iran na gargajiya na matasa ‘yan kasa da shekaru 23, ta lashe kambun duniya bayan da ta samu lambobin yabo mafi yawa. Kungiyar ta Iran ta sami lambobin zinariya 3, da azurfa 1 da kuma tagulla 2. ‘yan wasan da Iran da su ka sami kyautar zinariyar sun hada Iman Muhammadi mai ajin nauyi kilio 72, da Gulam Ridha Farakhi mai ajin nauyi kilo 87 da kuma Fardin Hidayati mai ajin nauyi 130. Wanda ya sami azurfa kuwa shi ne Sajjad Abbaspur mai ajin nauyi kilo 60, sai kuma wadanda su ka sami tagulla da su ne Ahamd Ridha Muhsin Najad mai ajin nauyi 67,sai Abul Fadal Muhmadim ai ajin nauyi 82. Kungiyar ta Iran ta...
Gwamnatin Jihar Sokoto ta amince a rika sauya kuɗaɗe da aka ware wasu wurare zuwa swasu idan can ya fi na farko amfani ga al’umma (virement) na naira biliyan 526 a cikin kasafin kuɗin shekarar 2025. Shugaban taron majalisar zartarwa ta jihar karo na 12 na bana, Gwamna Ahmad Aliyu, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa na da cikakken ƙuduri wajen gina Jihar Sokoto mai ingantaccen tattalin arziki ta hanyar aiwatar da muhimman sauye-sauye da shirye-shiryen ci gaban al’umma. Gwamna Aliyu ya bayyana cewa wannan sauyin kasafi an tsara shi ne domin ƙarfafa zuba jari a fannoni masu muhimmanci kamar gina manyan ayyukan raya kasa, inganta ayyukan jin kai, da haɓaka tasirin gudanar da ayyuka — ba tare da ƙara girman...
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce kasarsa za ta gwammace ta fuskanci takunkumin maimakon mika wuya ga manufofin ‘yan mulkin malla. “Mun cimma yarjejeniya da bangarori na Turai, amma ra’ayin Amurka ya bambanta, kuma abu ne na hankali kan cewa Iran ba zata mika wuya ga dukkanin abin da Amurka take bukata ba, domin hakan ya yi hannun riga da maslahar Iran. Amurka da kawayenta, wadanda ake kira da E3, sun ki amincewa da wani daftarin kuduri daga Rasha da China, wanda ya nemi jinkirta aiwatar da tsarin dawo da takunkumai kan Iran a karkashin yarjejeniyar nukiliya ta JCPOA. Pezeshkian ya kara da cewa Amurkawa “suna son mu ba su dukkan sinadarin uranium da aka tace, wanda ba za...
Fitaccen ɗan wasan tamaula, Lionel Messi, ya tsawaita kwantiraginsa da ƙungiyar Inter Miami har zuwa shekarar 2028, kamar yadda kulob ɗin ya sanar a ranar Alhamis, 23 ga Oktoba, 2025. Wannan sabon kwantiragin zai bai wa kulob ɗin da ma gasar MLS ta Amurka damar ci gaba da kasancewa tare da ɗaya daga cikin fitattun ’yan wasan da duniya ta taɓa gani har zuwa ƙarshen kakar wasa ta 2028. An kashe manoma uku da suke girbin amfanin gona a Filato Boko Haram sun kai sabbin hare-hare a wasu yankunan Borno da Yobe A ƙarshen wannan kakar ce kwataragin ɗan wasan na ƙasar Argentina zai ƙare, inda ya bayyana farin cikin sabunta shi kamar yadda wani saƙo da kulob ɗin ya...
Jagoran juyin juya halin musulunci na Iran wanda ya gana da tawagar masu shirya taron tunawa da Alamah Mirzai Na’ini ( R.A), ya ce; muhimman siffofi biyu da malamin ya kebanta da su, su ne kirkira a fagen ilimi da kuma a cikin ilimin siyasa. Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya bayyana Allamah Na’ini a matsayin daya daga cikin fitattun malamai, masu tarin sani a cikin jami’ar Najaf mai tsohon tarihi; jagoran juyin na Iran ya yi ishara da yadda marigayin malamin ya samar da ka’idojin da aka gina ilimin usulu akansu, wanda ya kai ga sabunta shi. Daga cikin rukunonin tunanin Allamah Na’ini kamar yadda jagoran juyin ya ambata da akwai batun kafa tsarin musulunci akan ginshikin wilaya domin kalubalantar...
Kungiyar gwagwarmyar ta Hamas ta yi maraba da matakin da kotun kasa da kasa ta ICJ ta dauka na karyata ikirarin da HkI ta yi kan hukumar bada agaji ga falsdinawa yan gudun hijira ta majalisar dinkin duniya . Gwamnatin Sahyuniya ta yi ikirarin karya kan hukumar ta UNRWA inda kafafen yada labarai na kasashen turai suka yayata ba tare da wani bincike ba kan gaskiyar lamarin, inda kotun ta ICJ ta majalisar dinkin duniya ta mayar da martani kan ikirarin karya da isra’ila ta yi kuma ta kare hukumar UNRWA ta bayyana irin ayyukan jinkai da take yi da gudanarwa ga alummar falasdinu. Babban kotun duniya ta umarci isra’ila da ta bada dama a shiga da kayayyakin agaji zuwa...
Sama da yahudawa 450 daga sassa daban daban na duniya ne suka yi kira ga majalisar dinkin duniya da sauran shuwagabannin kasashen duniya da su kakabawa gwamnatin Isra’ia takunkumin saboda kisan kare dangi da nuna rashin dan adamtaka da ta yi kan alummar gaza. Acikin wata budaddiyar wasika da suka rubuta sun bayyana cewa ba mu manta da cewa mafi yawancin dokoki da sharudda da kuma yarjeniyoyi da aka kafa an yi su ne don kiyaye da kuma kare rayukan yan adam, kuma don mayar da martani ga kisan yahudawa da aka yi na holocus. Wasikar ta bukaci a girmama hukumcin da kotun kasa da kasa ta fitar da ta hana aikawa da isra’ila makamai, sanya takunkumi ga duk wanda...
Aƙalla shugabanni 15 na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a Jihar Zamfara sun sauya sheka zuwa All Progressives Congress (APC). An gabatar da waɗannan waɗanda suka sauya shekar ne a gaban Ministan Harkokin Tsaro na Ƙasa, Dr. Bello Mohammed Matawalle, a Abuja ranar Laraba, ta hannun Shugaban APC na Jihar Zamfara, Alhaji Tukur Umar Danfulani, tare da Sanata Tijjani Yahaya Kaura da Alhaji Lawal M. Liman. A cewar wata sanarwa da Mai Magana da yawun jam’iyyar APC na Jihar Zamfara, Yusuf Idris Gusau, ya fitar, Minista Matawalle ya tarbi sabbin ’yan jam’iyyar da farin ciki, inda ya tabbatar musu da daidaito da damar ci gaba da aiki a cikin jam’iyyar. Dr. Matawalle ya bayyana matakin da suka...
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce tsarin zabe a Najeriya ya samu gagarumin ci gaba tun bayan da jam’iyyar PDP ta bar mulkin kasar a matakin tarayya. Akpabio, wanda aka zabe shi sau biyu a matsayin gwamna karkashin PDP kuma ya fara shiga majalisar dattawa a karkashin jam’iyyar, ya bayyana hakan ne a lokacin karatu na biyu a kan dokar gyaran tsarin zabe a zaman majalisa da aka yi a ranar Laraba. Dangote zai sayar da kaso 10 na hannun jarin matatar man shi NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Haraji Da Zai Fara Aiki A 2026 “Ina da tabbacin cewa ni da Sanata Abaribe, wanda muka shafe kusan shekaru 25 muna cikin...
Hon. Musa ya kara da cewa, aikin zai mayar da hankali ne kan nazari da binciken kimiyyar kasa a yankunan da ake tunanin cewa suna dauke da uranium, danyen man fetur, da iskar gas, da nufin tattara dukkan bayanan da ake bukata don ci gaba da aiki. A cewar kwamishinan, amincewar wani bangare ne na manufofin gwamnatin Gwamna Umar Namadi na binciko albarkatun ma’adanai na jihar don haɓaka tattalin arzikin cikin gida mai ɗorewa. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki October 22, 2025 Manyan Labarai Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi October 22, 2025 Da ɗumi-ɗuminsa ASUU Ta...
Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya ce matatar man shi na shirin sayar da tsakanin kashi 5 zuwa 10 cikin 100 na hannun jarinta a kasuwar hannun jari ta Najeriya. Ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da S&P Global, inda ya ce ana sa ran sayar da hannun jarin a cikin shekara mai zuwa. NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Haraji Da Zai Fara Aiki A 2026 Ko Alassane Ouattara zai samu wa’adi na 4 a mulkin Ivory Coast? Dangote ya ce wannan mataki kwatankwacin irin yadda aka gudanar sayar da hannun jarin kamfanononin siminta da suga na Dangote ne. “Ba ma son mu riƙe fiye da kashi...
Kotun kasa da kasa ta ICJ ta bayyana cewa Isra’ila ta karya dokokin kasashen duniya lokacin da ta hana shigar da kayan agaji ga Falasdinawa a Zirin Gaza. Kotun na mai bayyana cewa akwai wajabci kan Isra’ila na bayar da damar shigar da taimako cikin sauki zuwa yankin, sannan ya zama wajibi ta guji yin amfani da yunwa a matsayin makamin yaki. Kotun ta kuma bayyana cewa Isra’ila na da wajabcin hada hannu da kungiyoyin agaji na MDD, musamman Unrwa. Babban zauren MDD ne ya bukaci kotun ta bayyana ra’ayinta kan lamarin bayan da Isra’ila ta haramta ayyukan hukumar bayar da agajin jin kai ta falasdinawa cewa da Unrwa, tana mai zargin hukumar da hada kai da kungiyar Hamas. Share...
Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio ya yi gargadin cewa amincewar da majalisar dokokin Isra’ila ta yi na samar da kudirorin doka da nufin tsawaita ikon Isra’ila a gabar yammacin kogin Jordan “barazana ne ga yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza. Babban jami’in diflomasiyyar na Amurka ya shaidawa manema labarai a lokacin da yake shirin tafiya Isra’ila cewa, ” wannan ba wani abu ne da za mu iya ba da goyon baya gare shi ba a wannan lokaci.” Furin nasa na zuwa ne bayan da majalisar dokokin Isra’ila ta kada kuri’a kan samar da wani kudirin mallake Gabar Yamma da Kogin Jordan a matsayin yankin Isra’ila. Kudirin wanda wani dan majalisar Isra’ila mai tsattsauran ra’ayi ya gabatar na zuwa ne...
Majalisar tsarin mulki a Jamhuriyar Kamaru, ta ce sai zuwa ranar Litini 27 ga watan Oktoban nan ne za ta bayyana wanda ya yi nasara a zaben shugaban kasar. Majalisar ta sanar da ranar ne bayan ta duba tare da yin watsi da duk wasu kararrakin da suka shafi zaben na ranar 12 ga watan Oktoba. Kafin nan gwamnatin Kamaru ta haramta taron jama’a a birane da dama daga jiya Laraba, gabanin sanar da sakamakon zaben, biyo bayan da madugun ‘yan adawa na kasar Issa Tchiroma Bakary ya ayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar. Tun a makon da ya gabata ne magoya bayan Issa Tchiroma, wanda bisa ga kidayar tasa, ya ce ya samu kashi 54.8%...
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba A ranar 26 ga watan Yuni, shekara ta 2025, gwamnatin tarayya ta sanya hannu kan sabon tsarin haraji wanda za a fara aiwatarwa daga ranar 1 ga Janairu, 2026. Wannan sabon tsarin haraji na daga cikin matakan da gwamnati ke cewa zai taimaka wajen kara samun kudaden shiga da kuma rage dogaro da albarkatun mai. Sai dai, jama’a da dama ba su da cikakken bayani game da irin wadannan sabbin haraji ko menene suke nufi ba. NAJERIYA A YAU: Halin Da Muka Shiga Sakamakon Haihuwar ’Ya Mai Cutar Motsewar Kwakwalwa DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne? Shin ko ta wadanne hanyoyi ne wannan sabon haraji zai shafi rayuwar...
Tun daga lokacin da kasar Sin ta fara kera jiragen kasa masu saurin gudu a shekarar 2007 da samfurin CRH1 mai gudun kilomita 250 cikin sa’a guda, ba ta tsaya ba har zuwa yanzu da ta kera wannan sabon na zamani samfurin CR450 wanda shi ma an yi masa tsarin da za a ci gaba da inganta shi. Wannan fasaha wacce ta kara jaddada matsayin kasar Sin na ci gaba da zama jagora a fagen kere-keren jirgin kasa mafi gudu a duniya, ba kasar Sin kawai za ta amfanar ba har ma da sauran sassan duniya musamman a wannan zamani da kasar ta Sin ke kara bude kofarta ga kasashen waje da kuma neman cimma burin samar da al’umma mai...
Ya ce tallafin da Shugaba Tinubu ya amince da shi ba rance ba ne, wani bangare ne na yunkurin gwamnati na cire shingen da ke hana ’yan kasuwa ci gaba. Ya ƙara da cewa gwamnati ta kafa asusun Naira Biliyan 75 da sunan tallafin ga ƙananan masana’antu da yan kasuwa (MSME Intervention Fund), wanda ke bai wa ’yan kasuwa rancen har zuwa Naira miliyan 5 da kaso tara cikin ɗari (9%) a matsayin kudin ruwa, da kuma Naira biliyan 50 a ƙarƙashin shirin Shugaba kasa Bola Tinubu da ke bai wa ƙanana ’yan kasuwa tallafin kuɗi kyauta bisa wasu sharuɗɗa domin bunƙasa kasuwanci (Presidential Conditional Grant Scheme) da ke ba da tallafin Naira 50,000 ga ’yan kasuwa miliyan ɗaya...
Bam din Mark 84 kirar Amurka shi ne ya kashe dubunnan mutane a Gaza a hare-haren kisan kiyashi da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kai Bama-bamai na Mark 84 da Amurka ta kera ba su buƙatar karin haske, lallai sun kasance abin da ya fi daukar hankalin duniya a lokacin kazamin yakin da aka yi a zirin Gaza, saboda barnar da suka yi da kuma kashe-kashen jama’a da ba a taba gani ba. Wadannan bama-bamai su ne suka fi yaduwa a fagen yakin Gaza, kuma sun fi barna da halaka a lokacin da ake ci gaba da kai hare-hare kan al’ummar Gaza. Tunawa da su yana da alaƙa da mummunan kisan kiyashi da al’amuran zubar da jini da suka girgiza duniya....
Majalisar zartarwa ta jihar Jigawa ta amince da kashe Naira biliyan 2.55 domin gudanar da binciken na musamman, wanda zai mayar da hankali kan albarkatun mai, gas, da sinadarin uranium, tare da cikakken binciken kimiyyar kasa kan ma’adinai a fadin jihar. A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya fitar, ya bayyana cewa wannan muhimmin shiri na gwamnatin yanzu babban mataki ne na gaba wajen cika alkawarin gwamnati na ganowa da kuma amfani da albarkatun kasa masu tarin yawa da ke cikin jihar Jigawa. A cewarsa, wannan bincike zai samar da bayanai masu muhimmanci game da ma’adinai, da mmn fetur da iskar gas da ke karkashin kasa, wanda zai taimaka wajen yanke shawara mai...
Gwamnatin Jihar Kwara ta ware kimanin Naira Biliyan 8 da miliyan dari daya domin biyan haƙƙin fansho da giratuti na ma’aikatan jiha da na kananan hukumomi da suka yi ritaya. Kwamishinan Kuɗi na Jihar, Dakta Hauwa Nuhu, ce ta bayyana haka a yayin taro da ma’aikatun gwamnati karo na uku, wanda aka gudanar a zauren taro na ma’aikatar kuɗi a Ilori. A cewarta, za a raba Naira Biliyan biyar da miliyan dari shida ga tsoffin ma’aikatan jiha a matsayin giratuti, yayin da aka ware Naira Biliyan biyu da miliyan dari biyar domin tsoffin ma’aikatan kananan hukumomi. Dakta Nuhu ta jaddada cewa gwamnatin jiha za ta ci gaba da biyan fansho da giratuti a hankali domin tabbatar da cewa sauran ayyukan...
Piwuna, ya ce gwamnati ta gaza cika alƙawurran da ta ɗauka duk da sanarwar kwanaki 14 da ASUU ta bayar tun a ranar 28 ga Satumba, 2025. Ya ce babu wani abin da aka cimma wanda zai hana ƙungiyar aiwatar da shawarar majalisar zartarwarta na fara yajin aikin. “Dukkanin rassan ASUU a faɗin ƙasar nan an umarce su da su janye ayyukansu daga misalin ƙarfe 12 na dare ranar Litinin,” in ji Piwuna Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta kasa magance matsalolin cikin wannan lokaci, za ta ɗauki mataki mafi tsanani bayan kammala yajin aikin gargaɗin. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe...
Piwuna, ya ce gwamnati ta gaza cika alƙawurran da ta ɗauka duk da sanarwar kwanaki 14 da ASUU ta bayar tun a ranar 28 ga Satumba, 2025. Ya ce babu wani abin da aka cimma wanda zai hana ƙungiyar aiwatar da shawarar majalisar zartarwarta na fara yajin aikin. “Dukkanin rassan ASUU a faɗin ƙasar nan an umarce su da su janye ayyukansu daga misalin ƙarfe 12 na dare ranar Litinin,” in ji Piwuna Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta kasa magance matsalolin cikin wannan lokaci, za ta ɗauki mataki mafi tsanani bayan kammala yajin aikin gargaɗi. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe...
Shugaban kungiyar Hizbullah Ta Kasar Lebanon Sheikh Na’em Qasim ya bayyana cewa, ya bayyana cewa Firai ministan HKI Benyamin Natanyahu ya zubar da jinin mutanen yankin yammacin Asia da dama, amma wannan bai bashi lamunin cewa haramtacciyar kasar Isra’ila (HKI) zata zauna lafiya a yankin nan gaba ba. Tashar tal;abijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban kungiyar yana fadar haka a jiya Talata a wani bikin kaddamar da littafi wanda yake bayyana ra’yin Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminaie dangane da wakoki da kidekide. Yace: Duk tare da zubar da jinin mutanen yankin a duk a lokacinda ya ga dama, Netanyahu ba zai ce yana da lamuni na zaman lafiya ga HKI a nan...
A cikin jawabin da ya gabatar a wannan Talata da aka nuna kai tsaye a taron jana’izar babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Yemen Laftanar Janar Mohammed al-Ghamari, Sayyed Abdulmalik al-Houthi ya jaddada cewa, kasar Yemen za ta ci gaba da kasancewa cikin shirin komowa ga ayyukan soji idan Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta koma kisan kare dangi, da kuma ci gaba da killace yankin zirin Gaza. Sayyed al-Houthi ya yi ishara da irin babban gangami na dubban daruruwan mutane da suka taru a wurin jana’izar shahid al-Ghamari a matsayin abin da ke nuni da tsayin daka na al’ummar Yemen a kan manufofinsu. Sayyed al-Houthi ya kuma yi nuni da cewa al’ummar Yemen sun gamsu da matsayi mai Daraja da suke a...
Wasu da ake zargin masu kwacen waya ne sun kashe ma’aikaciyar jinya a Asibitin Gambo Sawaba da ke Zariya a jihar Kaduna mai suna Hadiza Musa. Bayanai sun ce marigayiyar it ace mataimakiyar shugabar sashen haihuwa a asibitin. Majalisa ta soma binciken yadda aka kashe $4.6bn na tallafin kiwon lafiya Gwamna Bala Mohammed ya ƙirƙiri sabbin masarautu 13 a Bauchi Mijinta, Hamza Ibrahim Idris, wanda ke aiki a Abuja, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an kashe matarsa ne a ranar Asabar yayin da take dawowa daga aiki. “A ranar Asabar, ta kira ni ta ce za ta je wajen gyaran gashi sannan ta ziyarci wani shagon masu magani a Filin Mallawa, Tudun Wada Zariya, kuma na amince.”...
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira biliyan ɗaya domin gyaran ajujuwan karatu a wasu makarantu na gwamnati. Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Dutse. A cewarsa, majalisar zartarwar jihar ta amince da kashe fiye da Naira miliyan 528 domin gyaran ginin ajujuwa a wasu zababbun makarantu na gwamnati a fadin jihar. Ya bayyana cewa, manufar aikin ita ce inganta yanayin karatu, tabbatar da tsaro, da kuma samar da iingantaccen ilimi karkashin shirin gwamnatin jihar na farfado da ilimin asali. Sagir Musa ya kuma ce, majalisar ta amince da kashe sama da Naira miliyan 512 domin samar...
“Wadanda aka nada sun bayyana a gaban kwamitin don tantancewa a ranar Talata, 14 ga Oktoba, 2025,” in ji shi. “Kwamitin bai samu koke ko korafe-korafe ba a kansu, sun nuna shiri da cancanta akan ayyukan da aka zabo su”. Ya bayyana sunayen wadanda aka tantance a matsayin: “Aminu Yusuf (Jihar Neja) – Shugaba, Joseph Haruna Kigbu (Jihar Nasarawa) – Kwamishina, Tonga Betara Bularafa (jihar Yobe) – Kwamishina. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi October 21, 2025 Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja October 21, 2025 Manyan...
Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya sanar da shirinsa na ɗaga darajar Kwalejin Jinya ta Nafisatu da ke Kwankwaso zuwa cikakkiyar Jami’ar Kiwon Lafiya albarkacin bikin zagayowar ranar haihuwarsa. Taron na wannan Talatar, 21 ga watan Oktoban 2025, ya gudana ne a garinsa na Kwankwaso da ke Karamar Hukumar Madobi, inda aka yaba da ci gaban da makarantar ta samu tun daga kafuwarta a 2019 zuwa yanzu. Tinubu ya naɗa sabon Minista Alƙaluman wucin-gadi na nuna Paul Biya ya lashe zaɓen Kamaru Kwankwaso ya ce an ɗauki wannan mataki ne domin ƙara buɗe damammaki ga mata matasa su sami ilimin kiwon lafiya mai zurfi. Ya jaddada cewa makarantar ita ce ta farko a Najeriya da ke karɓar dalibai...
Kasashen Iran da Iraki sun bukaci duniya da ta dakatar da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa Falasdinawa a Gaza Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da mai baiwa kasar Iraki shawara kan harkokin tsaro Qasim al-Araji sun bukaci kasashen duniya da su dakatar da kisan gillar da gwamnatin Isra’ila ke yi wa Falasdinawa a zirin Gaza. Al-Araji, wanda ke jagorantar wata tawagar jami’an tsaro a kasar Iran, ya gana da Araghchi a yammacin jiya Litinin, inda suka yi musayar ra’ayi da su kan hanyoyin inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, da kuma tattauna halin da ake ciki a Gaza da Lebanon. Dukkan jami’an biyu sun bayyana damuwarsu kan yadda Isra’ila ke ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita bude...
Bayanai daga Falasdinu na cewa a kalla Falasdinawa 97 ne sojojin Isra’ila suka kashe tare da jikkata wasu 230 tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta fara aiki a Gaza a ranar 10 ga watan Oktoba. A cikin wata sanarwa da ofishin yada labarai na gwamnatin Gaza ya fitar, ya ce ‘yan mamayar sun aikata laifuka 80 tun bayan ayyana tsagaita bude wuta, wanda hakan ya saba wa dokokin jin kai na kasa da kasa. Laifukan sun hada da harbin bindiga kai tsaye kan fararen hula da gangan, da kama fararen hula. A cewar sanarwar, sojojin na Isra’ila sun yi amfani da motocin soji, tankunan yaki da aka jibge a gefuna da wuraren zama, da jirage marasa, lamarin da...
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da aikin gina hanyar Babban Sara zuwa Malam Bako zuwa Shabaru zuwa Kirgi zuwa Albasu, mai tsawon kilomita 28.2, a Karamar Hukumar Sule Tankarkar,wanda kudinsa ya kakaNaira Biliyan 4.47, a ci gaba da shirin Gwamnati da Jama’a. Aikin hanyar zai hada fiye da kauyuka 60 tare da karfafa harkokin kasuwanci da zamantakewa a yankin. Haka kuma, gwamnan ya bude sabuwar cibiyar kula da lafiya ta farko, da makarantar Tsangaya ta zamani, da kuma rukunin samar da ruwa a yankin. Gwamna Namadi ya bayyana cewa shirin Gwamnati da Jama’a hanya ce ta karfafa gaskiya, bayyana ayyuka da kuma baiwa jama’a damar fadin ra’ayoyinsu. “Mun zo ne mu nuna abin da muka...
NLC ta kuma buƙaci gwamnati ta bi shawarar UNESCO wacce ta ke cewa ya kamata a ware aƙalla kashi 25 cikin 100 na kasafin kuɗi na kowace shekara ga ilimi. Ajaero, ya yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta kasa magance matsalolin cikin makonni huɗu, NLC za ta haɗa dukkanin ma’aikata na ƙasa don gudanar da yajin aiki na ƙasa baki ɗaya. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu October 21, 2025 Manyan Labarai Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara October 20, 2025 Manyan Labarai Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a October 20, 2025
Wata kotun majistare da ke Kano ta umarci Hukumar Hisbah ta jihar da ta shirya ɗaura aure tsakanin wasu fitattun ’yan TikTok guda biyu — Idris Mai Wushirya da Basira Yar Guda — cikin kwanaki 60. Kotun ta bayar da wannan umarnin ne bayan yaɗuwar bidiyon Mai Wushirwa da ’Yar Guda a kafafen sada zumunta, da Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta bayyana a matsayin “na batsa da rahsin tarbiyya.” Bidiyoyin sun nuna waɗannan ’yan TikTok ɗin suna nuna soyayya a bainar jama’a, abin da hukumomi suka ce ya saɓa da ɗabi’u da koyarwar addini da al’adun mutanen Jihar Kano. A yayin zaman kotun ranar Litinin, Mai Shari’a Halima Wali ta yi gargaɗi cewa idan ba a ɗaura auren...
Najeriya: ‘Yansanda A Abuja Sun Yi Amsani Da Hayakin Mai Sa Hawaye Kan Masu Neman A Saki Nnamdi Kanu
A jiya litinin ce masu goyon bayan Nnamdi Kanu shugaban kungiyar neman kafa kasar Biafara (IPOP) daga tarayyar Najeriya, wanda ake tsare da shugaban kungiyar tare da tuhumar ayyukan ta’addan sun fito zanga-zanga suka kuma tushe wata babban titi a Abuja. ‘Yansanda sun jefa masu hayakin teargas don tarwatse su a jiya litinin. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya bayyana cewa Kanu wanda yake da Passport na kasar Burtania ya yi kokarin wanke kansa daga tuhumar da ake masa tun 2021 amma ya kasa. Kanu yana jagorantar kungiyar IPOP tun da dadewa, da nufin samar da kasar Biafara a yankin kudu maso gabacin Najeriya. Kafin haka dai yan kabilar Ibo sun yi kokarin bellewa daga tarayyar Najeriya a...
Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arziki ta’annati ta samu nasarar tara dukiyar da ta haura naira biliyan 500 a tsawon shekaru biyu na gwamnatinsu. Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu, ya bayyana haka ne a yayin wani taron bita da ƙara wa juna sani na alƙalai da Hukumar EFCC tare da haɗin gwiwar Hukumar Shari’a ta Najeriya (NJC) suka shirya a birnin Abuja. Red Cross ta kafa cibiyoyin rage haɗurran bala’o’i a makarantun Gombe NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU Shettima ya buƙaci alƙalai da sauran ma’aikatan ɓangaren shari’a da su ƙara ƙaimi tare da yin aiki bisa gaskiya da adalci, yana mai...
Fitaccen jarumin barkwancin finafinan Indiyan nan Asrani ra rasu. Asrani, wanda asalin sunansa shi ne Govardhan Asrani, ya rasu yana mai shekaru 84, kuma ya shafe sama da shekara 50 yana fitowa a finafinan Indiya, inda ya fito a finafinai sama da 350. Dan wasan finafinan, ya shahara wajen taka rawar barkwanci da kuma ƙaramin jarumi wanda ake kira da mai taimaka wa jarumi wato supporting actor. Daga cikin fina-finansa da suka yi fice akwai Sholay, inda ya fito a matsayin ɗansand da Bawarchi da Chupke-Chupke da Hera Pheri da Muqabla da Dhamaal da Yamla Pagla Deewana da Dillagi da Welcome da Bhool Bhulaiya da Garam Masala da Baghban da The Burning Train da Ajnabee da Seeta aur Geeta da...
Wakilin Amurka Na Musamman A Siriya Ya Matsa Don Ganin Kasashen Saudiyya Da Lebanon Da Kuma Siriya Sun Kulla Alaka Da Isra’ila
Wakilin Amurka na Musamman a kasar Siriya ya matsa kaimi domin ganin kasashen Saudiyya da Lebanon da kuma Siriya sun kulla alakar jakadanci da haramtacciyar kasar Isra’ila Wakilin Amurka na musamman a Siriya Tom Barrack, ya gabatar da manufofinsa na sake fasalin yankin Gabas taTsakiya a siyasance bayan kawo karshen yakin Gaza. A cikin dogon hangen nesa, wanda ya wallafa a shafinsa na Twitter, Barrack ya yi ikirarin cewa abu mafi muhimmanci shi ne samar da zaman lafiya a yankin, da kwance damarar Hizbullah, da shigar da kasashen Labanon da Siriya cikin yarjejeniyoyin kyautata alaka da haramtacciyar kasar Isra’ila. Ya kara da cewa Saudiyya ma tana dab da kyautata alakarta da haramtacciyar kasar Isra’ila. Barrak ya bayyana cewa: Taron Sharm...
Hukumar gudanarwar Kungiyar Kwallon kafa ta Kano Pillars ta dakatar da Babban Kocinta Ahmed Garba Yaro Yaro da bai ba da shawara ga Kocin, Ogenyi Evans, nan take. Ta kuma nada tsohon kyaftin kuma Mataimakin Koci, Gambo Muhammad nan take, ya jagoranci lamuran fasaha na ƙungiyar. Mai horar da masu tsaron raga, Suleiman Shuaibu, zai taimaka masa, yayin da Koci Garzali Muhammad (Kusa) daga Junior Pillars zai ba da ƙarin goyon baya har sai an fitar da sabbin umarni. Kungiyar ta dauki wannan mataki ne bayan abin da ta kira “rashin tagomashinta” a Gasar Firimiyar Najeriya (NPFL) ta 2025/2026 da ake ci gaba da yi. Sanarwa da kulob ɗin ta fitar, hukumar gudanarwar ta ce an ɗauki matakin ne bayan...
Don haka, an nada “tsohon kaftin din kungiyar kuma mataimakin koci, Gambo Muhammad, tare da mai horar da masu tsaron gida, Suleiman Shuaibu, su maye gurbin wadanda aka sallama na dan wucin gadi. Bugu da kari, Koci Garzali Muhammad (Kusa) daga Junior Pillars zai taimakawa wadanda aka nada na dan wucin gadin”. LEADERSHIP ta ruwaito cewa, kungiyar mai taken ‘Sai Masu Gida’ tana fama a ‘yan makonnin nan. Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya ta kuma ci tarar kungiyar tarar kudi sama da Naira miliyan 9 biyo bayan rikicin da ya ɓarke a yayin da suke karawa da wata kungiya a filin wasa na Sani Abacha. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A...
Dakarun kare juyin musulunc na kasar iran ta bayyana cewa tana da cikakken shiri na kafa fadada dabarun yin hadin guiwa da dakarun karejuyin musulunci na kasar yamen wajen kalubalnatar kasashe ma’abota girman ai da kuma yan sahyuniya. A cikin sakon da kwamandan dakarun kare juyin musulunci na iran ya fitar a jiya lahadi mojor ganar mohammad pakpur ya aike da sakon ta’aziya ga babban hafsan hafsoshin sojin kasar Yamen brigadier janar Yousef hassan al’madani na shahadar major ganar mohammad abdular karin al’gamari wanda yayi fama da rashin lafiya sakamakon rauni da ya ji a harin da isra’ila ta kai masa a watan Augusta tare da wasu abokan aiki har da dan sa mai shakara 13. Har ila yau ya...
Darakta Janar na Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) Rafael Grossi ya bayyana kwarin gwiwar cewa, za a iya warware takkadama kan shirin Iran na makamashin nukiliya ne ta hanyar diflomasiyya kadai. Grossi ya bayyana hakan ne a wata hira da jaridar Neue Zeitung ta kasar Switzerland a jiya Lahadi. Shugaban hukumar ta IAEA ya ce, masu binciken ba su sami wata shaida da ke nuna cewa Iran ta boye wani adadi na sinadarin uranium da aka inganta ba. Ya kara da cewa, “Yawancin abubuwan da aka samu na Iran an adana su ne a wuraren da aka sani a Isfahan da Fordow, da kuma wani lokaci a Natanz.” in ji shi. Grossi ya bayyana kwarin gwiwa cewa “za a...
An saki ɗan jarida, Ibrahim Ɗan’uwa Rano, bayan da ƴansanda suka tsare shi a shalƙwatar Rundunar Ƴansanda ta Zone 1 Kano bisa zargin batanci ga wani mutum. Sakin nasa ya biyo bayan suka da matsin lamba daga ƙungiyoyin fararen hula irinsu Cibiyar Fasahar Bayanai da Ci Gaban Jama’a (CITAD), da Amnesty International, da sauran ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam, waɗanda suka bayyana tsarewar tasa a matsayin mataki na keta haƙƙin ɗan Adam da kuma yunƙurin danne ƴancin ƴan jaridu. Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya Ƙungiyoyin sun buƙaci a sake shi ba tare da wani sharaɗi ba, suna mai cewa tsarewar ta saɓawa...
Ƴansandan sun kuma yi kira ga ƴan jarida da su tabbatar da daidaito a rahotanninsu, tare da tuntuɓar sashin hulɗa da jama’a na yankin kafin yaɗa labaran da ke da sarƙakiya. AIG Garba ya gargaɗi ƴan jarida da su guji tsoma baki a cikin binciken da ke gudana, yana mai cewa “a bar doka ta yi aikinta.” Sai dai sanarwar ba ta fayyace halaccin tsarewar farko da aka yi wa ɗan jaridar ba, ko kuma ko an kama shi ne ba tare da takardar izinin kame ba. A halin yanzu, ƙungiyoyin kare ƴancin ƴan jarida da ƙungiyoyin farar hula da dama suna ci gaba da kira ga ƴansanda da su saki Ishaq tare da dakatar da duk wani yunƙuri na...
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana talauci a matsayin babban abokin gabar ɗan Adam. Ya ce ƙaruwar talauci a Najeriya na ci gaba da jawo rashin lafiya, jahilci, rashin tsaro, da rashin fata a tsakanin jama’a. ’Yan sanda sun tsare ɗan jarida kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook domin bikin Ranar Yaƙi da Talauci ta Duniya, Atiku, ya ce wannan rana tana tunatar da gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki muhimmancin ƙara ƙoƙari wajen yaƙar talauci “Talauci ne babban abokin gabar ɗan Adam. Yana haifar da matsaloli kamar rashin lafiya, jahilci, rashin tsaro da sauransu,” in...
Gwamnatin Tarayya ta ƙudiri aniyar rage kaso 30 cikin 100 na sinadarin gishiri (sodium) a kowane nau’in abincin ɗan fakiti da ake sayarwa a kantuna da wuraren kasuwanci a kasar. Aminiya ta ruwaito cewa gwamnatin za ta soma aiwatar da wannan shirin ne a bana domin daƙile cutar hawan jini da dangoginta a ƙasar. Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano An kama sojoji 20 kan yunƙurin kifar da gwamnatin Tinubu Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin lafiya kuma jakadiyar manufofin rage gishiri, Dokta Salma Ibrahim Anas, ce ta bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar a fadar shugaban kasa yayin bikin Ranar Abinci ta Duniya ta 2025 a Abuja. A cewarta,...
Yanzu kuma za a ci gaba da tattaunawa kan yadda za a aiwatar da sauran sharuddan da ke ke kunshe a yarjejeniyar. Masu sanya ido na ganin cewa aikin sake ginan yankin Gaza wanda aka rushe kusan daukacinsa a yakin da aka yi na shekara biyu, zai zama babban kalubale. Wannan ce ranar da kowa ke jira -Trump A lokacin da Donald Trump ya yi jawabi, ya bayyana yau a matsayin “ranar da kowa ya yi ta hankoro da addu’ar ganin zuwan ta.” Shugaban na Amurka ya ce “Wannan yarjejeniya mai matukar tarihi” wadda gungun shugabannin duniya suka sanya wa hannu, na nuna cewa “addu’ar miliyoyin al’umma ta karbu”. Daga nan sai ya ce shugabannin sun samu nasarar...
Ofishin Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sanar a ranar Asabar cewa “Mashigar Rafah a Gaza za ta kasance a rufe har sai abin da hali ya yi a nan gaba.” Ofishin Netanyahu ya kara da cewa, bude mashigar ya dogara ne bisa ga yadda Hamas ta aiwatar da tsarin yarjjeniyar da aka cimmawa wajen mika gawawwakin Isra’ilawa da ke hannunta. Wannan bayanin ya zo ne jim kadan bayan da ofishin jakadancin Falasdinu a Masar ya sanar da cewa za a sake bude mashigar Rafah da ke kudancin zirin Gaza a ranar Litinin mai zuwa. A nata bangaren, kungiyar Hamas ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, matakin da Netanyahu ya dauka yana a matsayin keta sharuddan yarjejeniyar tsagaita bude...
A wani jawabin da aka yada ta kafar sadarwar zamani ta shafin Facebook jiya, ma’aikatar ta kara da cewa tun lokacin da shi Gwamnan ya dare kan Kujerar mulkin Jihar, mulkin gwamna Inuwa ya kafa dokar ta baci kan lamarin daya shafi ilimi, inda ya bullo da tsare tsare da zuba jari da zummar bunkasa bangaren ilimiin. Wadanda za su amfana da karin tallafin kudin karatun sun hada dalibai masu karatun da suka hada da PhD, MSc, PGD, BSc, HND, NCE, ND, da kuma Satifiket. Da yake na shi jawabin wajen sa albarkacin baki kan ci gaban da aka samu, Shugaban kungiyar dalibai ‘yan asalin Jihar da suke Jami’ar Jihar Gombe, Abubakar Muhammad Yamanga, ya bayyanawa LEADERSHIP cewa...
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Kuduri mai lamba 2231 ya ƙare aiki a yau A cikin wata wasika da ya aike wa babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da shugaban kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, ministan harkokin wajen kasar Iran ya tabbatar da cewa a karshe kuduri mai lamba 2231 ya kare a yau, kuma duk wani kira na farfado da shi ko dawo da wa’adin kudirorin da ya kare, ba shi da wani tushe na shari’a, kuma ba zai iya haifar da wani tasiri na tilasta aiki da shi ba. Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Sayyid Abbas Araqchi ya aike da wasika zuwa ga babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da kuma shugaban kwamitin sulhu...
Shi ma a nasa jawabin yayin gudanar da taron, shugaban kwamitin Alhaji Abdullahi Abdulmalik Digi, ya ce, a shekaru hudu da ya yi yana jagorancin kwamitin sun yi abin da yakamata su yi, inda ya ce, a Azumin bara an dauki yara marayu 2000 da aka raba musu abinci da suka hada da buhunan shinkafa da kuma kayan Sallah da za su dinka, mata aka raba musu shadda mata kuma atamfofi inda jimillar kudin da aka kashe ya zama Naira miliyan 64.2. Bayan wannan an kashe Naira milin 26 wajen biya wa yara 520 kudin makaranta, inda kowane yaro ake biya masa Naira dubu 50 a kananan hukumomi shida na FCT Abuja. Sannan an kashe Naira miliyan 3...
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar adawa a Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, ya yi iƙirari cewa ministoci da manyan hafsoshin sojin ƙasar sun taya shi murnar bayan bayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka kammala. Issa Tchiroma Bakary ya bayyana cewa ministoci da manyan jami’an tsaron da ministocin sun kira shi a waya suna jaddada goyon bayansu da niyyar biyayya ga kundin tsarin mulkin ƙasar da kuma abin da al’umma suka zaɓa. Ya bayyana haka ne wani a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, yana mai nuna godiya ga waɗanda suka goyi bayansa, tare da jaddada cewa wannan lokaci yana da muhimmanci matuka ga kasa. Ya ce, “Ina godiya daga zuciyata ga ministoci...
A yayin da Najeriya ke karkata zuwa amfani da kayan tsaro na zamani na cikin gida domin ƙarfafa gwiwar jami’an tsaronta a fagen fama, wani ɗan Jihar Katsina ya fara ƙera motar yaƙi nau’in Track Armored Personnel Carrier (TAPC). Jihar Katsina na daga cikin jihohin Arewa da suka fi fama da hare-haren ’yan bindiga, inda suka kashe dubban mutane tare da raba wasu da muhallansu gami da rusa harkokin tattalin arziki da na zamantakewa. Ana cikin haka ne wani ɗan asalin yankin Kaita a jihar mai suna Injiniya Ibrahim Lawal Ɗankaba, ya fara yunƙurin ƙera motar yaƙi, wadda ya sanya wa suna Beguwa, a ƙoƙarinsa na tallafa wa yunƙurin gwamnati na daƙile ayyukan ’yan ta’addanci da suka daɗe suna...
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta fidda bayani kan cewa daga yau Asabar 18 ga watan Octoban shekara ta 2025, kudurin kwamitin tsaro na MDD wanda aka samar don goyon bayan aiwatar da yarjeniyar Nukliyar kasar Iran wacce aka fi sani da JCPOA ya kawo karshe. Don haka daga yau shirin Nukliyar kasar Iran ta koma karkashen yarjeniyar NPT, kuma za’a yi mu’amala da shirin kamar sauran kasashen karkashin kula na hukumar IAEA. Tsahar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ma’aikatar na bada wannan sanarwan a safiyar Asabar ta kara da cewa dama kudurin na tsawon shekaru goma ne daga yau ta gama aiki. Daga yau shirin Nukliyar JMI zai ci gab aba tare da wani karin ka’idojin...
Kauyukan kasar Iran guda uku, Soheili a kan tsibirin Qeshm, da Kandelous a lardin Mazandaran, da kuma Shafiabad a lardin Kerman na kasar Iran sun shiga cikin zababbun kauyuka a duniya na yawon shekatawa saboda kyauwunsu da kuma samar da dukkan abin kyautata rayuwa a cikinsu. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto mataimakin ministan al-adu na kasar Iran yana bada wannan sanarwan a jiya Jumma’a. Anoushirvan Mohseni-Bandpei, ya kara da cewa zabar wadan nan kauyuka na kasar Iran cikin kyauyuka wadanda suka cancanci shiga wuraren yawon shakatawa a duniya wanda hukumar ‘ The United Nations World Tourism Organization (UNWTO), ta yi zai bunkasa yawon shakatawa a kasar Iran , kuma ma’aikatarsa tana aiki dare da rana don...
Tashar talabijin ta CNN ta bayar da rahoton cewa, Janar Alvin Holsey, kwamandan rundunar sojin Amurka ta Kudu, ya yanke shawarar yin murabus nan da watan Disamba, saboda takun-saka tsakaninsa da sakataren tsaron Pete Hegseth, kan rashin jituwar da aka samu game da batun ayyukan sojojin Amurka a yankin Caribbean. Rahoton ya bayyana cewa, a makwannin da suka gabata ne Janar Holsey ya bayyana damuwarsa kan sahihancin wadannan ayyuka, yayin da Hegseth ya nuna takaicinsa kan yadda ayyukan ke tafiyar hawainiya, lamarin da ya janyo cece-kuce tsakanin bangarorin biyu. A cewar rahoton, manyan jami’an biyu sun tayar da jijiyoyin wuya ne a yayin wani taro a ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon a makon da ya gabata, inda suka yi musayar...
Tawagar sun gabatar da kansu ga babban sakataren hukumar gudanarwar ci gaban Jihar Katsina, Dakta Mustapha Shehu. Tawagar sun ce ziyarar wani bangare ne na shirye-shiryen gudanar da aikace-aikace domin inganta zaman lafiya da kuma sanar da tallafin jin kai ga ‘yan gudun hijira. Gwamnan Katsina ya yaba wa Bankin Duniya da ya yi hadin gwiwa da Jihar Katsina don fuskantar matsalolin tsaro da kuma tallafa wa ‘yan gudun hijira. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja October 17, 2025 Rahotonni Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya October 17, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu...
Abokan Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya Sun Ce: Sake Dawo Da Takunkumin Da Aka Kakaba Kan Iran Baya Kan Doka
Abokan Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya sun bayyana cewa: Sake dawo da takunkumi bayan karewarsa baya da wani tushe na doka ko tsari Kungiyar aminan Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da wata sanarwa game da cikar kudiri mai lamba 2231 kan yarjejeniyar makamashin nukiliyar Iran a ranar 18 ga watan Oktoba, inda ta bayyana cewa matakin da Amurka da Turai suka dauka na sake daukar matakin kakaba takunkumin da ya kare kan wata kasa tsari ne da baya ya kan wani tushe na doka ko yarjejeniyar kasa da kasa. Kungiyar aminan Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da wata sanarwa a ranar Alhamis da ke nuna cikar kuduri mai lamba 2231 na kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya...
Majalisar Zartarwar Jihar Jigawa ta amince da wasu manyan kwangiloli da kudinsu ya haura Naira Biliyan 6, domin karfafa bangarorin noma, ilimi da ci gaban tattalin arziki a fadin jihar. A cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai bayan zaman majalisar da aka gudanar a fadar gwamnatin Dutse, kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya bayyana cewa wannan mataki na nuna kudirin gwamnatin jihar wajen inganta muhimman bangarori da ke da tasiri kai tsaye ga rayuwar al’umma. A cewarsa, majalisar ta amince da kashe sama da Naira biliyan 2 domin sayen babura nau’in Hunter guda 1,180 ga malaman gona a fadin jihar. Ya ce wannan mataki ya yi daidai da kokarin Gwamna...
A taron majalsar zartarwar, Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa zabinsa na Amupitan ya yi ta’allaka ne a kan rashin nuna son kai na siyasa, gaskiya da kyakkyawan tarihinsa. Mambobin majalisar, ciki har da shugabanni na yanzu da na baya, sun amince da nadin, suna bayyana Farfesa Amupitan a matsayin mutum mai gaskiya. Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya ce tarihin Amupitan na ciki da kwazo da adalci da kwarewa da hidimar kasa. Bayan amincewar majalisar, ana sa ran shugaba zai mika sunan Amupitan zuwa majalisar dattawa don tantancewa da tabbatarwa bisa ga tsarin kundin mulkin Nijeriya. Farfesa Amupitan, mai shekaru 58, dan asalin kauyen Ayetoro Gbede a cikin karamar hukumar Ijumu ta Jihar Kogi. Ya...
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar iran Ismail Baqaei yayi maraba da dakatar da bude wuta da aka yi tsakanin kasashen Pakistan da Afghanistan, kuma yayi kira ga kasashen biyu da su warware sabanin dake tsakanin ta hanyar tattaunawa da kuma diplomasiya. Iran ta dade tana ba da shawarwarin magance matsalolin tsaro a yammacin Asiya da kuma Kudancin Asiya, da kuma nuna rashin amincewa kan tsoma bakin kasashen waje kan rashin fahimtar dake tsakanin kasashen musulimi, yace rikicin dake tsakanin Kabul da islam abad barazana ce ga zaman lafiya yankin, kuma zai amfanar da kungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi masu so su yi amfani da tarzoma a iyaka. Rikicin kan iyaka tsakanin Pakistan da Afghanistan yayi Kamari a yan kwanakin nan inda...
Rahotanni sun bayyana cewa shakih Naim Qassim babban sakatare janar din hizbullah na kasar labanon ya bayyana a jiya Alhamis a gaban mambobin kungiyar Kashafat Al-Mahadi cewa Amerika da Isra’ila ba za su iya yin galaba akan hizbullah ba, Babban hadafin kafa wannan kungiyar shi ne kokarin wayar da kan yara matasa yan shekara 6 zuwa 18 muhimman alamuran addini, adaidai lokacin da gwamntin sahyuniya take ta kokari wajen yada akidar sahyuniyanci tsakanin yara matasa, kungiyar tana taka muhimmiyar rawa wajen yada akidar gwagwarmaya ga matasa masu tasowa inda yanzu haka tana da mambobin fiye da 100,000. Shaikh Naim Qaseem ya bayyana muhimmancin wannan kungiyar kuma ya bayyana cewa samuwar wadannan matasa zai kara taimakawa wajen tunkarar dukkan kalubalen dake...
Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, Shugaba Tinubu ya yi wa akasarinsu sassauci ne, bisa rahotannin da ke cewa; wadanda aka yanke wa hukuncin, sun nuna matukar nadama da kuma halin kirki. Haka zalika, ya yafe wa wasu saboda tsufa da samun sabbin fasahohin sana’o’i, ko shiga Jami’ar NOUN. Shugaba Tinubu ya kuma gyara rashin adalcin tarihi, wanda Turawan mulkin mallaka na Burtaniya suka yi wa Sir Herbert Macaulay, daya daga cikin masu kishin kasa a Nijeriya. A takaice dai, kwamitin bai wa shugaban kasa shawara, kan jinkai, karkashin jagorancin babban mai shari’a; kuma ministan shari’a, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi, ya bayar da shawarar yin afuwa ga fursunoni biyu da 15 da aka yankewa hukunci, wadanda 11 daga cikinsu sun...
Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka Ta Bar Baya Da KuraAfuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka Ta Bar Baya Da Kura
Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, Shugaba Tinubu ya yi wa akasarinsu sassauci ne, bisa rahotannin da ke cewa; wadanda aka yanke wa hukuncin, sun nuna matukar nadama da kuma halin kirki. Haka zalika, ya yafe wa wasu saboda tsufa da samun sabbin fasahohin sana’o’i, ko shiga Jami’ar NOUN. Shugaba Tinubu ya kuma gyara rashin adalcin tarihi, wanda Turawan mulkin mallaka na Burtaniya suka yi wa Sir Herbert Macaulay, daya daga cikin masu kishin kasa a Nijeriya. A takaice dai, kwamitin bai wa shugaban kasa shawara, kan jinkai, karkashin jagorancin babban mai shari’a; kuma ministan shari’a, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi, ya bayar da shawarar yin afuwa ga fursunoni biyu da 15 da aka yankewa hukunci, wadanda 11 daga cikinsu sun...
Kasar Saudiyya ta rage yawan guraben kujerun aikin hajjin da take ware wa Najeriya daga 95,000 zuwa 66,910 daga shekarar 2026. Aminiya ta ruwaito cewa a baya Najeriya ta shafe tsawon shekaru uku tana samun guraben na 95,000 a yayin Aikin Hajjin. ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 8 a harin kwanton ɓauna a Zamfara An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi A cewar Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), wannan sauyi ya biyo bayan gazawar Najeriya wajen cika guraben da aka ware mata a hajjin shekarun 2024 da 2025. Wata sanarwa da, Mataimakiyar Darakta a Sashen Yaɗa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara, ta sanya wa hannu, ta ce hakan na nufin za...
A yammacin jiya Alhamis ne sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani ya gana da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin a birnin Moscow inda ya isar da sakon jagoran juyin juya halin musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ga shugaban na Rasha. Bangarorin biyu sun tattauna batutuwa da dama da suka hada da huldar dake tsakanin kasashen biyu, da hadin gwiwar tattalin arziki, da ci gaban yankin, da kuma sauran batutuwa na kasa da kasa. A makon da ya gabata, Putin ya ce mahukuntan Isra’ila sun bukaci ya isar da sako ga Iran cewa ba su niyar sake kaddamar da wani hari a kan kasar ta Iran. “Muna ci gaba da samun sakonni daga jagorancin Isra’ila suna neman...
Hakazalika, ta bai wa mata 30 masu kananan sana’o’i tallafin buhun gawayi, da kilo 10 na Shinkafa da litar man girki. Bugu da kari, ga kungiyoyi shida na mata manoma, kowacce za ta karɓi fanfunan feshi, famfun ruwa, da kuma maganin feshin ciyawa. Hajiya Shema’u, ta yaba da karuwar adadin mata a harkar noma, inda ta ce, manoma mata da suka yi rajista da NAWIA a yanzu sun haura 2000, yayin da wadanda ba su yi rajista ba sun kai 5,000. Shemau ta kuma mika godiyarta ga Uwargidan gwamnan jihar Zamfara, Hajjiya Hurriya Dauda bisa namijin kokarin da take yi na bunkasa noman mata a Jihar Zamfara. Sauran hukumomin da kungiyoyin da suke tare da NAWIA...
Sashen kashe radadi domin gudanar da aikin tiyata ga marasa lafia na asibitin gwamnatin tarayya FMC da ke garin Birnin Kudu a jihar Jigawa ya gudanar da bikin ranar bada maganin radadi ta duniya ta bana. Kungiyar ma’aikatan bada maganin kashe radadi dan yin aikin tiyata ta Duniya ce ta kebe ranar 16 ga wata Oktobar kowacce shekara domin bikin wannan rana. Shekaru 170 ke nan da fara amfani da maganin kashe radadi, inda wasu likitoci su ka yi gwajin wannan magani a asibitin birnin Massachusetts na kasar Amurka, abin da ya kawo sauyi wajen yi wa marasa Lafia aikin tiyata daga shekara 1846. Malam Aliyu Umar Yusuf na sashen bada maganin kashe radadi na asibitin gwamnatin tarayya FMC...