Aminiya:
2025-12-13@13:59:05 GMT

Ina son komawa Barcelona kafin na yi ritaya — Messi

Published: 10th, November 2025 GMT

Fitaccen ɗan wasan ƙasar Argentina, Lionel Messi, wanda yanzu haka yake taka leda a ƙungiyar Inter Miami ta Amurka, ya bayyana burinsa na sake komawa Barcelona kafin ya yi ritaya daga tamaula, domin yin bankwana da masoyansa.

Messi ya bayyana hakan ne yayin ziyarar da ya kai filin wasan Camp Nou da aka yi wa gyare-gyare, inda ya ce ya yi matuƙar kewar filin da kuma magoya bayan ƙungiyar ta Catalonia.

An kashe mayaƙa 200 a rikicin Boko Haram da ISWAP ’Yan bindiga sun sace mata 5 a Kano

A cikin saƙon da ya wallafa a shafinsa na Instagram a ranar Litinin, ɗan wasan mai shekaru 38 ya ce: “Na yi kewar wannan fili ƙwarai. Ina fata wata rana zan dawo in sake taka leda a nan gaban masoyana kafin in yi ritaya.”

A shekarar 2021 Messi ya bar Barcelona bayan matsalolin kuɗi da suka dabaibaye kulob ɗin, inda ya koma Paris Saint-Germain (PSG) ta Faransa, kafin daga bisani ya sauya sheƙa zuwa Inter Miami ta Amurka bayan shekaru biyu.

Messi, wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or har sau takwas, ya ƙara da cewa ziyarar da ya kai Camp Nou ta sake jaddada masa irin farin cikin da yake ji a duk lokacin da yake wannan fili.

“Camp Nou wuri ne da yake sa ni farin ciki matuƙa. Ina fatan zan dawo ba wai kawai don yin bankwana ba, har ma don sake taka leda a matsayin ɗan wasa.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barcelona

এছাড়াও পড়ুন:

Osimhen Ya Lashe Kyautar Gwarzon Dan Wasan Kwallon Kafa Na Bana A Kasar Turkiyya

Hukumar kwallon kafa ta Nigeria (NFF) ta taya Osimhen murnar samun wannan babbar nasarar a kwallon kafa ta hanyar sanya hoton Osimhen a babban shafinsu na Facebook da yake da mabiya fiye da miliyan daya, Osimhen na daga cikin yan wasan da kocin tawagar ta Super Eagles Eric Chelle ya gayyata domin buga gasar kofin kasashen Afirka da za a buga a Morocco a shekara mai zuwa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Salah Ba Ya Cikin ‘Yan Wasan Liverpool Da Za Su Kara Da Inter Milan December 8, 2025 Wasanni Shirye-shiryen Fara Kofin Afirka: Abin Da Ya Kamata Ku Sani December 7, 2025 Wasanni Liverpool Ba Ta Yi Min Adalci Ba – Muhammad Salah December 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya
  • Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699
  • Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina
  • Osimhen Ya Lashe Kyautar Gwarzon Dan Wasan Kwallon Kafa Na Bana A Kasar Turkiyya
  • Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.
  • Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025