Aminiya:
2025-11-10@18:08:24 GMT

Ina son komawa Barcelona kafin na yi ritaya — Messi

Published: 10th, November 2025 GMT

Fitaccen ɗan wasan ƙasar Argentina, Lionel Messi, wanda yanzu haka yake taka leda a ƙungiyar Inter Miami ta Amurka, ya bayyana burinsa na sake komawa Barcelona kafin ya yi ritaya daga tamaula, domin yin bankwana da masoyansa.

Messi ya bayyana hakan ne yayin ziyarar da ya kai filin wasan Camp Nou da aka yi wa gyare-gyare, inda ya ce ya yi matuƙar kewar filin da kuma magoya bayan ƙungiyar ta Catalonia.

An kashe mayaƙa 200 a rikicin Boko Haram da ISWAP ’Yan bindiga sun sace mata 5 a Kano

A cikin saƙon da ya wallafa a shafinsa na Instagram a ranar Litinin, ɗan wasan mai shekaru 38 ya ce: “Na yi kewar wannan fili ƙwarai. Ina fata wata rana zan dawo in sake taka leda a nan gaban masoyana kafin in yi ritaya.”

A shekarar 2021 Messi ya bar Barcelona bayan matsalolin kuɗi da suka dabaibaye kulob ɗin, inda ya koma Paris Saint-Germain (PSG) ta Faransa, kafin daga bisani ya sauya sheƙa zuwa Inter Miami ta Amurka bayan shekaru biyu.

Messi, wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or har sau takwas, ya ƙara da cewa ziyarar da ya kai Camp Nou ta sake jaddada masa irin farin cikin da yake ji a duk lokacin da yake wannan fili.

“Camp Nou wuri ne da yake sa ni farin ciki matuƙa. Ina fatan zan dawo ba wai kawai don yin bankwana ba, har ma don sake taka leda a matsayin ɗan wasa.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barcelona

এছাড়াও পড়ুন:

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko November 8, 2025 Wasanni Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax November 6, 2025 Wasanni Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe mayaƙa 200 a rikicin Boko Haram da ISWAP
  • An sake rage kuɗin aikin Hajjin 2026 a Najeriya
  • Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL
  • Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya
  • Kungiyar Hadin Kai Ta Kafin Hausa Ta Horas Da Matasa 160 Sana’o’in Hannu
  • Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
  • Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 
  • Dan Wasan Taekwando Na Kasar Iran Abulfazl Zandi Ya Zamo Shi Ne Na Daya A Duniya
  • Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna