Gwamna Soludo ya lashe Zaɓen Anambra karo na biyu
Published: 9th, November 2025 GMT
Charles Soludo na jam’iyyar All Progressives Grand Alliance wato APGA, ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Anambra wanda aka yi a jiya Asabar, 8 ga watan Nuwamba.
Baturen zaɓen jihar, Farfesa Edoma Omoregie ne ya sanar da sakamakon a cibiyar tattara sakamakon zaɓen da ke babban birnin jihar, Awka a safiyar yau Lahadi.
Ya ce Soludo ya samu ƙuri’a 422,664, sai kuma Nichola Ukachukwu na jam’iyyar APC mai biye masa da ƙuri’a 99,445.
George Moghalu na jam’iyyar Labour ne ya zo na uku da ƙuri’a 10,576, sai Jude Ezenwafor na PDP mai ƙuri’a 1401.
Charles Soludo wanda tsohon shugaban babban bankin Najeriya ne, ya lashe zaɓen ne domin yin sake mulkin jihar a karo na biyu.
Hukumar ta wallafa sakamakon zaɓen ne a shafin intanet na musamman mai suna IReV, kamar yadda Dokar Zaɓe ta 2022 ta tanada.
Tun da farko dai INEC ta sanar da sakamakon a hedikwatarta da ke Awka a hukumance, amma ta ce tana gudanar da lissafin ƙarshe na alƙaluman kafin ta ayyana Charles Soludo a matsayin wanda ya lashe zaɓen.
Bitar sakamakon da hukumar ta fitar a hukumance ta nuna cewa ta hanyar lashe zaɓe a duk ƙananan hukumomi 21, Charles Soludo ya riga ya wuce ƙa’idar Kundin Tsarin Mulki don haka za a ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen.
Duk da cewa zaɓen ya kasance cikin kwanciyar hankali a faɗin jihar, akwai damuwa game da siyan kuri’u, yayin da hukumar EFCC ta ce jami’anta sun kama mutane uku da ake zargi da sayen kuri’u a lokacin zaɓen.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Charles Soludo jihar Anambra ya lashe zaɓen Charles Soludo
এছাড়াও পড়ুন:
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal
Ya ƙara da cewax gwamnatinsa ta fara gyara daga tushe, inda ilimi ya zama ginshiƙin farko. “Shekaru takwas kafin mu hau mulki, ɗalibanmu ba su samun takardun WAEC, sannan tsawon shekaru biyu suna fama da matsalar NECO. Na biya Naira Biliyan huɗu don magance wannan matsala,” inji shi.
Gwamnan ya bayyana irin matsalolin da ya gada, yana mai cewa: “Na samu asusun gwamnati da naira miliyan huɗu kacal. Ma’aikata suna karɓar albashi cikin rashin tabbas, babu ruwa, asibitoci kuwa suna cikin mummunan yanayi.”
Lawal ya ce, ya sake fasalin tsarin gwamnati, inda ya rage yawan kwamishinoni da manyan sakatarorin don rage ɓarna da ƙara inganci. “Yanzu muna daga cikin jihohi mafi ci gaba wajen tara haraji, inda kuɗaɗen shiga suka ƙaru da fiye da kaso 300 cikin 100,” inji shi.
Ya bayyana cewa gwamnatin sa ta gina ko ta gyara makarantu sama da 500, tare da aiwatar da ayyukan da kuɗinsu ya kai biliyan N10 a kowace ƙaramar hukuma. Duk da cewa ana cire biliyan 1.2 a kowane wata daga kuɗaɗen gwamnati don biyan basussuka, an biya bashin fansho da giratuti na fiye da biliyan N13.6 da aka tara tun shekarar 2011.
A ɓangaren tsaro, Lawal ya ce jihar ta ɗan sami sauƙi bayan kafa rundunar tsaron gida, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin tabbatar da amfanin mulki ya kai ga talaka.
A nasa jawabin, Babban Editan LEADERSHIP, Azu Ishiekwene, ya ce an bai wa gwamnan wannan lambar yabo ne saboda irin nasarorin da ya samu a fannonin tsaro, ilimi, lafiya da gine-gine, yana mai cewa “jarida tana da alhakin duba gwamnati, amma kuma tana da haƙƙin yabawa idan ana yin daidai.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA