Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-01@04:46:20 GMT

FMC Birnin Kudu Ya Yi Bikin Ranar Maganin Kashe Radadi Ta Duniya

Published: 16th, October 2025 GMT

FMC Birnin Kudu Ya Yi Bikin Ranar Maganin Kashe Radadi Ta Duniya

Sashen kashe radadi domin gudanar da aikin tiyata ga marasa lafia na asibitin gwamnatin tarayya FMC da ke garin Birnin Kudu a jihar Jigawa ya gudanar da bikin ranar bada maganin radadi ta duniya ta bana.

Kungiyar ma’aikatan bada maganin kashe radadi dan yin aikin tiyata ta Duniya ce ta kebe ranar 16 ga wata Oktobar kowacce shekara domin bikin wannan rana.

Shekaru 170 ke nan da fara amfani da maganin kashe radadi, inda wasu likitoci su ka yi gwajin wannan magani a asibitin birnin Massachusetts na kasar Amurka, abin da ya kawo sauyi wajen yi wa marasa Lafia aikin tiyata daga shekara 1846.

Malam Aliyu Umar Yusuf na sashen bada maganin kashe radadi na asibitin gwamnatin tarayya FMC da ke garin Birnin Kudu ya ce taken ranar bikin na bana shi ne “Muhimmancin aikin kashe radadi a yanayin da ake bukatar agajin gaggawa” abin da yasa su ka yi amfani da wannan dama wajen shirya bita ga jami’an hukumar kiyaye hadura na karamar hukumar Birnin kudu kan hanyoyin lalubo numfashin wanda ya suma saboda bugun zuciya ko hadarin mota.

Da ya ke gabatar da bitar a aikace, Shugaban Sashen bada maganin kashe radadi lokacin aikin tiyata na asibitin gwamnatin tarayya dake Birnin kudu, Dakta Oliwe Augustus Chuks, ya ce akwai matakai da dama da ake bi wajen lulubo numfashin wanda ya yanke jiki ya fadi sumamme.

Yana mai cewar wadannan hanyoyi sun hada da tabbatar da yiwuwar bada agajin gaggawa lami lafia kafin taba jikin maras lafiya, da neman taimakon jama’a dan ceton rai da kuma danna kirjin wanda ya suma a hankali dan jini ya gudana daga zuciya zuwa kwakwalwa.

Yace sai kuma hura iska a baki domin bude kafofin da su ka toshe da motsa kashin mukamuki dan bude kofofin shan iska wadda hakan zai kai ga dadowar numfashi.

Sai dai kuma Likitan ya yi kira ga jama’a a tashar mota da makarantu da gidaje da su lakanci dabarun lalubo numfashin wanda ya suma domin kuwa wannan ilimi bai takaita ga likitoci kadai ba har ma da gamagarin mutane dan ceto rai kafin zuwa asibiti.

A nasa bangaren, Jami’in hukumar kiyaye hadura ta kasa na karamar hukumar Birnin Kudu, Malam Shu’aibu Uba Baba, ya bayyana jin dadin sa bisa wannan bita da ma’aikatan bada maganin kashe radadi lokacin aikin tiyata na asibitin FMC da ke garin Birnin Kudu su ka shirya musu.

Ya lura cewar, bitar za ta sake inganta abin da su ka sani wajen bada agajin gaggawa lokacin hadarin mota, inda ya roki ma’aikatan asibitin da su ware lokaci domin ci gaba da yi musu irin wannan bita nan gaba.

Taron ya samu halartar kungiyar kiyaye hadura ta masu yiwa kasa hidima, inda aka bada damar tambayoyi da bada amsa yayin da wasu daga cikin ma’aikatan hukumar kiyaye hadura da na masu yiwa kasa hidima suka jarraba matakan da likitocin su ka koyar da su muraran a aikace.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa bada maganin kashe radadi da maganin kashe radadi kiyaye hadura aikin tiyata

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda mutane suka yi cikar ƙwari don halartar jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi

Dubban mutane sun taru a Jihar Bauchi, don halartar jana’izar fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya rasu a ranar Alhamis a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa.

Gwamnatin Jihar Bauchi, ta ayyana ranar Juma’a a matsayin ranar hutu domin ba jama’a damar halartar jana’izar malamin.

Trump zai haramta wa ’yan Najeriya da wasu ƙasashe zuwa Amurka CAF Tayi Watsi Da Alƙalan Wasan Nijeriya a Kofin Afrika Na 2025

Ɗalibansa da sauran Musulmi daga Bauchi da maƙwabtan jihohi sun isa da wuri domin halartar jana’izar.

Huumomi sun tsaurara matakai a jihar don tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali.

Maulud Dahiru Bauchi, wanda ya yi magana a madadin iyalan marigayin, ya ce za a yi jana’izar malamin da misalin ƙarfe 3 na rana bisa wasiyyar malamin.

Ya ƙara da cewa Sheikh Sharif Saleh ne zai jagoranci jana’izar.

Jama’a da dama sun halarta, ciki har da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, gwamnoni, sarakuna, ’yan kasuwa, attajirai da sauransu.

Iyalan mamacin sun ce dandazon mutanen da suka halarci jana’izar, ya nuna tasirin da Sheikh Dahiru ya yi wajen yaɗa addini da tarbiyya tsawon rayuwarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
  • An yi gangami a fadin duniya a zagayowar ranar Falasdinu
  • Trump Ya Bada Sanarwan Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venezuela Gaba Daya
  • Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
  • DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali
  • Asibitin Kula Da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa Na Kaduna Na Bunƙasa Ta Fannoni Daban-Daban
  • Yadda mutane suka yi cikar ƙwari don halartar jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Ƙasar Japan ta fara sayar da injin da ke yi wa mutane wanka
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 10 A Wani Hari Da Ta Kai A Birinin Damaskas Na Kasar Siriya