Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia
Published: 7th, November 2025 GMT
’Yan sanda a kasar Indonesia sun ce an garzaya da daruruwan mutane zuwa asibiti bayan wani abu da ake zargin bam ne ya fashe a wani masallacin Juma’a da ke Jakarta babban birnin kasar.
Lamarin ya faru ne a lokacin sallar Juma’a a cikin wani ginin makaranta da ke Kelapa Gading, a arewaci Jakarta.
Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800Kwamishinan ’yan sandan birnin, Asep Edi Suheri, ya ce har yanzu ana bincike don gano musabbabin fashewar.
Shaidun gani da ido sun ce sun ji fashewa biyu masu ƙarfi da misalin ƙarfe 12 na rana a agogon kasar, daidai lokacin da aka fara hudubar sallar Juma’a a masallacin.
Suheri ya ce an kai mutane 54, galibinsu ɗalibai zuwa asibiti da raunuka masu sauƙi da masu tsanani, ciki har da wadanda suka kone.
Ya ƙara da cewa mutum 20 na ci gaba da samun kulawa a asibiti, inda uku daga cikinsu ke fama da raunuka masu tsanani.
Suheri ya ce ƙungiyar ƙwararrun masu binciken bama-bamai da aka tura wurin ta gano bindigogin wasa da ƙaramar bindiga ta wasa a kusa da masallacin.
“’Yan sanda na ci gaba da binciken wurin don gano musabbabin fashewar,” in ji shi.
Kafafen yaɗa labarai na cikin gida a kasar sun nuna bidiyon da ke nuna layin ’yan sanda da ke kewaye da makarantar, inda motoci masu ɗaukar marasa lafiya ke tsaye a gefe.
Sai dai hotunan masallacin ba su nuna wata mummunar lalacewa ba sakamakon harin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Harin bam
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano
An kama mutum biyu ’yan jam’iyyar NNPP a Karamar Hukumar Tofa da ke Jihar Kano, kan sukar Shugaban Karamar Hukumar, Ibrahim Yakubu Addis, a Facebook.
Wadanda da aka kama sun hada da Murtala Garba Doka da Shamsu Safiyanu Lambu wanda aka fi sani da Shamzeet Lambu.
Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwaRahotanni sun bayyana cewar shugaban karamar hukumar ne ya bayar da umarnin kama su ne a ranar Litinin.
Shamzeet Lambu ya wallafa a Facebook, inda ya zargi shugaban karamar hukumar da kin kammala aikin titin Lambu zuwa Banki zuwa Yarimawa da Jakata, wanda gwamnatin jiha ta amince da shi kan kudi kimanin naira miliyan 240.
A rubutun da ya wallafa cikin harshen Hausa, Lambu ya ce: “Naira miliyan 240 kudinmu a Burji, Allah Ya saka mana.”
Rahotanni sun nuna cewa an fara tsare mutanen biyu a ofishin ’yan sanda na Tofa, kafin daga bisani aka mayar da su hedikwatar rundunar da ke kwaryar birnin Kano a Bompai domin ci gaba da bincike.
Shugaban matasa na yankin, Kwamared Nazifi Ado Lambu, ya tabbatar da kamen, inda ya ce hakan ya tayar da hankalin jama’a a yankin.
“E, an kama su saboda rubutun da suka yi a Facebook game da aikin titi. An tsare su a Tofa kafin daga bisani aka kai su Bompai,” in ji shi.
Wani mazaunin Lambu, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce al’ummar yankin sun dade suna rokon shugaban karamar hukumar kan gyara titin.
“Ya taba yin alkawarin zai gina titin da bututun ruwa da kwalta, amma bayan gwamnatin jiha ta amince da aikin, sai aka tsaya a iya share titi da zuba yashi, sai kuma aka bar aikin,” in ji mazaunin.
Da aka tuntubi shugaban karamar hukumar, Ibrahim Yakubu Addis, ya ce shi ne ya kai kara ofishin binciken laifuka (CID) domin a tabbatar da gaskiyar zargin da ake yi masa.
“Ba mu yi musu komai ba illa tambayarsu su kawo hujjar zargin da suka yi. Mutane da yawa suna ganin abin da ake wallafawa a intanet, kuma ba wannan ne karo na farko da suke irin wannan ba,” in ji shi.
Ya kuma ce adadin kudin aikin da suke zargi ba gaskiya ba ne.
“Gwamna ya amince da aikin da kudi kasa da Naira miliyan 100, ba miliyan 240 ba.
“Mun dai ce su kawo hujja kawai,” in ji shugaban.
Kamen mutanen biyu ya haifar da ce-ce-ku-ce a Karamar Hukumar Tofa, inda jama’a ke kira da a warware lamarin cikin lumana.