Hakazalika, ta bai wa mata 30 masu kananan sana’o’i tallafin buhun gawayi, da kilo 10 na Shinkafa da litar man girki.

 

Bugu da kari, ga kungiyoyi shida na mata manoma, kowacce za ta karɓi fanfunan feshi, famfun ruwa, da kuma maganin feshin ciyawa.

 

Hajiya Shema’u, ta yaba da karuwar adadin mata a harkar noma, inda ta ce, manoma mata da suka yi rajista da NAWIA a yanzu sun haura 2000, yayin da wadanda ba su yi rajista ba sun kai 5,000.

 

Shemau ta kuma mika godiyarta ga Uwargidan gwamnan jihar Zamfara, Hajjiya Hurriya Dauda bisa namijin kokarin da take yi na bunkasa noman mata a Jihar Zamfara.

 

Sauran hukumomin da kungiyoyin da suke tare da NAWIA sun hada da Zamfara Chambers of Commerce, ACRESAL, NG-CARES, LIPAN, LP PRESS da kuma Nigeria Export Promotion Council (NEPC).

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa October 16, 2025 Labarai Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara October 16, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC October 16, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

FMC Birnin Kudu Ya Yi Bikin Ranar Maganin Kashe Radadi Ta Duniya

Sashen kashe radadi domin gudanar da aikin tiyata ga marasa lafia na asibitin gwamnatin tarayya FMC da ke garin Birnin Kudu a jihar Jigawa ya gudanar da bikin ranar bada maganin radadi ta duniya ta bana.

Kungiyar ma’aikatan bada maganin kashe radadi dan yin aikin tiyata ta Duniya ce ta kebe ranar 16 ga wata Oktobar kowacce shekara domin bikin wannan rana.

Shekaru 170 ke nan da fara amfani da maganin kashe radadi, inda wasu likitoci su ka yi gwajin wannan magani a asibitin birnin Massachusetts na kasar Amurka, abin da ya kawo sauyi wajen yi wa marasa Lafia aikin tiyata daga shekara 1846.

Malam Aliyu Umar Yusuf na sashen bada maganin kashe radadi na asibitin gwamnatin tarayya FMC da ke garin Birnin Kudu ya ce taken ranar bikin na bana shi ne “Muhimmancin aikin kashe radadi a yanayin da ake bukatar agajin gaggawa” abin da yasa su ka yi amfani da wannan dama wajen shirya bita ga jami’an hukumar kiyaye hadura na karamar hukumar Birnin kudu kan hanyoyin lalubo numfashin wanda ya suma saboda bugun zuciya ko hadarin mota.

Da ya ke gabatar da bitar a aikace, Shugaban Sashen bada maganin kashe radadi lokacin aikin tiyata na asibitin gwamnatin tarayya dake Birnin kudu, Dakta Oliwe Augustus Chuks, ya ce akwai matakai da dama da ake bi wajen lulubo numfashin wanda ya yanke jiki ya fadi sumamme.

Yana mai cewar wadannan hanyoyi sun hada da tabbatar da yiwuwar bada agajin gaggawa lami lafia kafin taba jikin maras lafiya, da neman taimakon jama’a dan ceton rai da kuma danna kirjin wanda ya suma a hankali dan jini ya gudana daga zuciya zuwa kwakwalwa.

Yace sai kuma hura iska a baki domin bude kafofin da su ka toshe da motsa kashin mukamuki dan bude kofofin shan iska wadda hakan zai kai ga dadowar numfashi.

Sai dai kuma Likitan ya yi kira ga jama’a a tashar mota da makarantu da gidaje da su lakanci dabarun lalubo numfashin wanda ya suma domin kuwa wannan ilimi bai takaita ga likitoci kadai ba har ma da gamagarin mutane dan ceto rai kafin zuwa asibiti.

A nasa bangaren, Jami’in hukumar kiyaye hadura ta kasa na karamar hukumar Birnin Kudu, Malam Shu’aibu Uba Baba, ya bayyana jin dadin sa bisa wannan bita da ma’aikatan bada maganin kashe radadi lokacin aikin tiyata na asibitin FMC da ke garin Birnin Kudu su ka shirya musu.

Ya lura cewar, bitar za ta sake inganta abin da su ka sani wajen bada agajin gaggawa lokacin hadarin mota, inda ya roki ma’aikatan asibitin da su ware lokaci domin ci gaba da yi musu irin wannan bita nan gaba.

Taron ya samu halartar kungiyar kiyaye hadura ta masu yiwa kasa hidima, inda aka bada damar tambayoyi da bada amsa yayin da wasu daga cikin ma’aikatan hukumar kiyaye hadura da na masu yiwa kasa hidima suka jarraba matakan da likitocin su ka koyar da su muraran a aikace.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci
  • FMC Birnin Kudu Ya Yi Bikin Ranar Maganin Kashe Radadi Ta Duniya
  • Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona
  • Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi
  • Hukumar Kula Da GIdajen Gyaran Hali A Zamfara Ta Neman Shigarda Fursunoni Tsarin Inshorar Lafiya Na NHIS
  • ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako
  • Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
  • Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya
  • Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata