Daga Usman Muhammad Zaria

Gidauniyar Tunawa da Marigayi Sir Ahmadu Bello (ABMF) ta yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa sauƙin kai, tawali’u da jajircewarsa wajen ci gaban Jihar Jigawa.

Shugaban Kwamitin Amintattu na Gidauniyar kuma tsohon Gwamnan Jihar Neja, Dr. Mu’azu Babangida Aliyu ne ya yi wannan yabon yayin da ya jagoranci tawaga zuwa gaisuwar ban girma a fadar gwamnatin jihar da ke Dutse.

Ya ce salon jagoranci na Gwamna Namadi na ɗauke da ƙima da marigayi Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato, ya shahara da su, musamman tsari, girmama jama’a da shugabanci na gaskiya da rikon amana.

Dr. Aliyu ya yi kira ga shugabannin Arewa su rungumi jagoranci da ke maida hankali kan al’umma, tare da fifita ilimi a matsayin tubalin cigaba.

Ya kuma sanar da cewa Jihar Jigawa ce za ta karbi bakuncin taron gidauniyar na shekarar 2026, wanda zai ƙunshi laccoci, shirye-shiryen wayar da kan jama’a da bada lambar yabo.

A jawabinsa, Gwamna Namadi ya gode wa Gidauniyar bisa wannan yabo da kuma zaɓar Jigawa don karɓar taron na 2026.

Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da bin sawun Sardauna ta hanyar shugabanci na gaskiya, tsare-tsaren jin daɗin jama’a da kuma zuba jari a fannin ilimi.

Ya tabbatar da cikakken goyon baya wajen shirya taron 2026 cikin nasara.

Tawagar ta haɗa da Madakin Zazzau, Malam Muhammad Munir Ja’afaru, da wasu jami’an Gidauniyar.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti

Kwamandan Ƙungiyar sa kai ta Vigilante Group of Nigeria (VGN) reshen Jihar Kaduna, Abdulwahab Muhammed ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta amince da Ƙungiyar a matakin ƙasa ta hanyar sanya hannu a kan ƙudurin da aka gabatar.

A cewar ƙungiyar bisa la’akari da irin rawar da take takawa wajen daƙile ayyukan miyagu da samar da tsaro a sassan ƙasar nan.

An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa

Ya ce lokaci ya yi da gwamnati za ta sa hannu kan kudurin amincewa da kungiyar domin kasancewa cikin jerin hukumomin tsaro na kasa, la’akari da irin jajircewar da suke nunawa musamman a Jihar Kaduna.

Abdulwahab ya bayyana hakan ne yayin taron ƙarin girma da ƙungiyar ta shirya ga wasu jami’anta a Ƙaramar hukumar Jama’a, inda kuma aka karrama wasu fitattun mutane da ke ba da gudunmawa wajen tallafa wa ayyukan tsaro.

Kwamandan ya ce, suna da kyakkyawar fahimta da haɗin kai da sauran jami’an tsaro, inda suke miƙa waɗanda suka kama ga ’yan sanda don gudanar da bincike da yin hukunci bisa doka. Ya roƙi gwamnatin jihar Kaduna da ta ƙara tallafa musu da kayan aiki domin sauƙaƙa gudanar da ayyukansu.

Shi ma Shugaban karamar hukumar Jama’a Peter Tanko Dogara wanda sakataren Ƙaramar hukumar Jama’a, Dakta Shehu Usman Danbala ya wakilta, ya yaba da ƙoƙarin ƙungiyar wajen tabbatar da tsaro a matakin sa kai, tare da kiran al’umma da su riƙa basu cikakken goyon baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Don Yaki da Laifuffuka A Maiduguri
  • Za A Gudanar Da Taron Masana Harkokin Yada Labarai Karo Na 2 A Kano
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Farmaki Ga Wani Dan Majalisa A Jihar Niger