Ban ɓata zargin Shettima da ƙirƙiro Boko Haram ba — Sheriff
Published: 8th, November 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa ya taɓa zargin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, da ƙirƙiro Boko Haram.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Sanata Sheriff ya bayyana labarin a matsayin ƙarya mara tushe.
Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar NajeriyaYa ce bai taɓa yin wata hira ko yi wa wani bayani da ya shafi Shettima game da kafa Boko Haram ba.
“Wannan labari ƙarya ne gaba ɗaya, kuma an shirya shi ne domin rikita jama’a da kawo rabuwar kai,” in ji sanarwar.
Sheriff, wanda tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, ya ce waɗanda suka yaɗa wannan labari suna ƙoƙarin rage ƙimarsa da kuma ɓata gudunmawar da yake bayarwa wajen samar da zaman lafiya da haɗin kai a Jihar Borno da Najeriya baki ɗaya.
Ya ce ya umarci lauyoyinsa su gano waɗanda suka yaɗa labarin tare da ɗaukar matakin shari’a a kansu.
“Idan ba a gaggauta goge wannan labari daga kafafen da suka yaɗa shi ba, zan ɗauki matakin shari’a,” in ji Sheriff.
Sanata Sheriff, ya roƙi ’yan Najeriya da kafafen watsa labarai da su yi watsi da labarin, tare da bin gaskiya da adalci wajen yaɗa bayanansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram rahotanni zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
Wata kotu a Ƙasar Jamus ta yanke wa wani ma’aikacin jinya hukuncin ɗaurin rai da rai bayan ta same shi da laifin kashe marasa lafiya 10 da kuma yunƙurin kashe ƙarin wasu 27 ta hanyar yi musu allurar guba.
Kotun da ke birnin Aachen a yammacin Jamus, ta tabbatar da cewa mutumin mai shekaru 44 ya aikata laifukan ne tsakanin watan Disamban 2023 zuwa Mayun 2024 a asibitin Wuerselen.
Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a IndonesiaKotun ta bayyana cewa laifin da ya aikata babban laifi ne, wanda zai hana shi samun ’yanci bayan shekaru 15 kamar yadda ake yadda a irin waɗannan shari’o’in.
Ba a bayyana sunan mutumin ba, amma masu gabatar da ƙara sun ce yana “wasa da rayuwar marasa lafiyar” da yake kula da su.
Lauyansa ya roƙi kotu ta wanke shi lokacin da aka fara shari’ar a watan Maris.
Masu gabatar da ƙara sun ce mutumin yana yi wa marasa lafiya, waɗanda mafi yawansu tsofaffi ne, allurar magunguna masu sa barci da rage zafi don rage wahalar aikinsa a lokacin dare.
Sun kuma bayyana cewa mutumin yana da matsalar halayya, ba ya nuna tausayawa ga marasa lafiya, kuma bai nuna nadama ba a lokacin shari’ar.
Haka kuma, sun ce yana amfani da morphine da midazolam, wani magani da ake amfani da shi a wasu lokuta wajen aiwatar da hukuncin kisa a Amurka.
An kuma sake zarginsa da yin aiki ba tare da bin ƙa’ida ba, da kuma rashin nuna ƙwazo a aikinsa.