Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai
Published: 5th, November 2025 GMT
Sakamakon kwamitin, wanda ke dauke da kusan shafuka 40 ya bayyana shawarwari kan gyare-gyare da matakan da za a dauka na gaggawa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio November 5, 2025
এছাড়াও পড়ুন:
Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu
Kungiyoyin da suka yi hadin gwiwar shigar da karar sun hada da Interfaith Partners for Peace and Development, Fityanul Islam of Nigeria, Sairul Qalbi Foundation, Tijjaniyya Youth Enlightenment Initiative, Hablullahi Mateen Foundation, Dariqa Qadiriyya of Nigeria, Kadiriyya Youth Awareness, Kadiriyya Riyadul Janna Kofar Na’isa, Ashabul Kahfi Foundation, da Majmau Ashabul Yameen.
LEADERSHIP ta ruwaito cewa, takaddamar da ta shafi Malam Lawan Triumph ta fara ne a watan Satumba bayan da wasu ƙungiyoyin addini suka ɗauki wasu wa’azozinsa a matsayin ɓatanci ga Annabi SAW, wanda ya haifar da cece-kuce da muhawara a faɗin jihar. Wannan lamari ya sa gwamnatin jihar ta shiga tsakani ta hannun Majalisar Shura ta Jiha, wadda aka ba da umarnin gudanar da bincike kan zarge-zargen.
Bisa umarnin gwamnati, Majalisar Shura bayan ta tantance wa’azozin malamin, sannan daga baya ta gayyace shi don zaman tattaunawa.
Tun bayan zaman, har zuwa yanzu babu wata sanarwa a hukumance daga gwamnati kan sakamakon zaman da kwamitin Shura ya yi akan Malam Triumph.
Har zuwa lokacin rubuta wannan rahoton, gwamnatin Jihar Kano ko rundunar ‘yansanda ba su bayar da wani martani a hukumance kan karar ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA