Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil
Published: 7th, November 2025 GMT
Bugu da kari, a gefen taron na COP30, Ding ya gana da sakatare-janar na Majalisar Dinkin Duniya Mista Antonio Guterres. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Za A Gudanar Da Taron Masana Harkokin Yada Labarai Karo Na 2 A Kano
Daga Khadijah Aliyu
An fara shirye-shirye gudanar da taron shekara-shekara karo na 2 da bikin shigar da sabbin mambobi na Ƙungiyar Masana Harkokin Yada Labarai ta Najeriya (SNB), bayan an kaddamar da Kwamitin Shirya Taron (LOC) a Kano.
An tsara gudanar da taron ne daga ranar 20 zuwa 21 ga watan Nuwamban 2025.
Shugaban Ƙungiyar, Farfesa Umaru A. Pate, ya umarci kwamitin da ya gudanar da aikinsa da himma da jajircewa domin tabbatar da nasarar taron, wanda shi ne irinsa na farko da za a yi a Kano.
Ya bayyana cewa ana sa ran masana sama da 400 da sabbin mambobi daga ciki da wajen jihar za su halarta.
Farfesa Pate ya yaba wa Gwamnatin Jihar Kano kan jajircewarta wurin inganta aiki da ɗabi’a a harkar yada labarai, yana mai cewa taron zai kasance muhimmiyar dama wacce za ta ƙara ɗaukaka martabar jihar a fagen kafofin yaɗa labarai.
A nasa jawabin, Shugaban LOC, Alhaji Ado Salisu Warawa, ya nuna godiya ga jagorancin ƙungiyar na ƙasa bisa amincewa da kwamitin, yana mai tabbatar da cewa za su gudanar da taron cikin cikakkiyar nasara.
Rel/Khadijah Aliyu