Daga cikin ƙorafe-ƙorafen da masu ƙara suka zayyana sun haɗa cewa, ya danganta halittar Annabi SAW da ƙasƙantun halittu (‘Ya’yan Tumkiya, da Karya, da Ƙwarƙwata), sannan kuma ya taɓa alfarmar iyayen Annabi SAW wanda a cewarsu, hakan bai dace ba a alfarmarsa fiyayyen halitta.

 

Gwamnatin Kano, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ba tare da ɓata lokaci ba, ta miƙa koken ga Majalisar Shura ta jihar domin fayyace gaskiyar lamari.

 

Majalisar Shura, ta bakin Sakatarenta, Shehu Wada Sagagi, a wani taron manema labarai da ta gudanar, ta tabbatar da cewa, za ta gudanar da cikakken bincike akan zargin da aka yi wa Malamin (Abubakar Triumph). Sannan kuma, za ta gayyaci masu ƙorafe-ƙorafe da kuma Malamin domin sauraron bayanansu. Ya ce matakin zai bai wa kowanne ɓangare dama kuma za a bi ƙa’idojin shari’ar Musulunci wajen gudanar da binciken.

 

Sagagi ya roƙi jama’a da su zauna cikin kwanciyar hankali, tare da jaddada muhimmancin kiyaye zaman lafiya da Kano ta yi fintinƙau akai. Ya tabbatar da cewa, majalisar za ta yi bincike da tattaunawa kafin ta bai wa gwamnati shawara kan matakin da ya dace bisa ga ƙa’idar shari’a.

 

Daga bisani kuma, rahotanni sun bayyana cewa, Majalisar ta dakatar da Malam Abubakar Triumph daga yin wa’azi a jihar har sai ta kammala bincike.

 

Ta kuma yi gargaɗi ga ‘yan siyasa da su guji tsoma baki a lamarin, inda ya jaddada buƙatar barin Majalisar ta kammala aikinta cikin gaskiya da adalci.

 

Ranar da aka daɗe ana tsumayi, ranar zaman tattaunawa da Malam Triumph da masu sukar kalamansa, ta tabbata inda aka yi zama a ofishin Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da ke Kano a ranar Litinin, 13 ga watan Oktoban 2025.

 

An gudanar da taron ne ƙofa rufe, inda mambobin Majalisar suka shawarci malamin da ya riƙa yin taka-tsantsan da natsuwa a cikin bayanansa na addini. Rahotanni sun nuna cewa, malamin ya nemi afuwa a yayin tattaunawar.

 

Bayan kammala zaman, Malam Triumph ya wallafa kalmar “Alhamdulillah” a shafinsa na Facebook abin da jama’a da dama suka fassara a matsayin alamar cewa an kammala zaman lafiya tsakaninsa da Majalisar Shura, amma dai, al’umma musamman masu ƙorafi suna nan suna jiran sakamakon zaman tattaunawar daga bakin gwamnatin Kano.

 

Ko ina aka kwana? Majalisar Shura ba ta miƙa sakamakon zaman ba ne ga gwamnatin Kano ko kuma gwamnatin ce ta yi biris?

 

Don jin wannan amsar ne, masu ƙorafi a ƙarƙashin ɗariƙun sufaye suka maka gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da kwamishinan ‘yansanda na jihar a kotu kan zargin cewa, sun ƙi gudanar da haƙƙin da ya rataya a kansu kan cafke wanda ake zargi da yin ɓatanci ga Annabi Muhammad SAW.

 

An ga matakin kotun ne a wata takarda da aka yada a kafafen sada zumunta, mai taken “Dambarwar Shari’a a cikin batun Malam Abubakar Lawal (Lawan Triumph) a Babbar Kotun Shari’a ta Jihar Kano.”

 

A cewar takardar, waɗanda ake ƙara da suka haɗa da Gwamna Yusuf, Kwamishinan ‘Yansanda, da Babban Lauyan gwamnati, an zarge su da gazawa wajen aiwatar da ayyukansu na doka na gurfanar da masu aikata manyan laifuka a ƙarƙashin Dokar Shari’a ta Jihar Kano ta 2000 da Dokar Laifukan Intanet ta 2024 (wadda aka yi wa kwaskwarima).

 

Ƙungiyoyin da suka yi haɗin gwiwar shigar da ƙarar sun haɗa da Interfaith Partners for Peace and Development, Fityanul Islam of Nigeria, Sairul Qalbi Foundation, Tijjaniyya Youth Enlightenment Initiative, Hablullahi Mateen Foundation, Dariqa Qadiriyya of Nigeria, Kadiriyya Youth Awareness, Kadiriyya Riyadul Janna Kofar Na’isa, Ashabul Kahfi Foundation, da Majmau Ashabul Yameen.

 

Har zuwa lokacin rubuta wannan nazari, gwamnatin Jihar Kano ko rundunar ‘yansanda ba su bayar da wani martani a hukumance kan ƙarar ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya November 8, 2025 Manyan Labarai Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi November 8, 2025 Manyan Labarai Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10 November 8, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Shura gwamnatin Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano

Wani yaro ɗan shekara biyu mai suna Danjuma Salman, ya rasu bayan ya faɗa cikin rijiya a Jihar Kano.

Lamarin ya faru ne a Ƙaramar Hukumar Gwale.

Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa

Rahotanni sun nuna cewa yaron ya zame ne sannan ya faɗa cikin rijiyar wadda murfinta ya lalace.

Mai magana da yawun Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya bayyana cewa sun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 10:05 na safe daga wani mai suna Saminu Dayyabu, wanda ya sanar da su cewa wani yaro ya faɗa cikin rijiyar.

“A lokacin da jami’anmu suka isa wajen, sun tarar da yaro ɗan shekara biyu, Danjuma Salman, wanda ya faɗa cikin wata rijiya da murfinta ya lalace,” in ji sanarwar.

Abdullahi, ya ce jami’an hukumar sun fito da yaron, amma daga bisani aka tabbatar da rasuwarsa.

An miƙa gawar yaron ga mahaifinsa, Salman Dayyabu, bayan an fito da shi daga rijiyar.

Daraktan Hukumar Kashe Gobara na jihar, Alhaji Sani Anas, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyayen yaron.

Ya kuma yi kira ga mazauna unguwanni da su riƙa rufe rijiyoyi da sauran wuraren ruwa yadda ya kamata domin guje wa irin wannan iftila’i.

Haka kuma ya shawarci iyaye da su riƙa kula da yaransu sosai, musamman a wuraren da ke da hatsari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ban taɓa zargin Shettima da ƙirƙiro Boko Haram ba — Sheriff
  • Ban ɓata zargin Shettima da ƙirƙiro Boko Haram ba — Sheriff
  • Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko
  • Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita