An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou
Published: 5th, November 2025 GMT
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE November 5, 2025
Daga Birnin Sin Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka November 5, 2025
Daga Birnin Sin CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika November 5, 2025
এছাড়াও পড়ুন:
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya
A yau Talata ne firaministan Sin Li Qiang, ya gana da kakakin majalisar wakilan tarayyar Najeriya Tajudeen Abbas, wanda ya isa birnin Shanghai don halartar baje kolin CIIE karo na takwas.
Yayin zantawarsu, Li Qiang ya bayyana aniyar kasar Sin ta karfafa salon wanzar da ci gaba bisa manyan tsare-tsare tare da Najeriya, da zage damtse wajen aiwatar da wasu muhimman matakai goma na bunkasa kawance tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka, da hada hannu wajen gina shawarar “Zira Daya Da Hanya Daya” mai inganci, da bunkasa matakin hadin gwiwa a sassan gargajiya, da fadada hadin gwiwa a sabbin masana’antu, da kara kyautata gina tattalin arziki da zamantakewar al’ummun sassan biyu.
Li Qiang ya kara da cewa, akwai bukatar kasashen biyu su karfafa tsare-tsare, da hadin gwiwa a fannin gudanar da cudanyar mabambantan sassa, karkashin irinsu hadakar kasashen BRICS, da MDD, da yayata hadin kai, da inganta karfin kasashe masu tasowa.
A nasa tsokacin, Tajudeen Abbas ya ce Najeriya na rike da manufar nan ta Sin daya tak a duniya, kuma a shirye take ta karfafa musayar kwarewar jagoranci tare da Sin, da fadada hadin gwiwa a sassa da dama, kamar tattalin arziki da cinikayya, da samar da ababen more rayuwa, da makamashi, da al’adu, tare da ci gaba da daga cikakkiyar dangantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Najeriya da Sin zuwa babban matsayi. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA