An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano
Published: 6th, November 2025 GMT
An kama mutum biyu ’yan jam’iyyar NNPP a Karamar Hukumar Tofa da ke Jihar Kano, kan sukar Shugaban Karamar Hukumar, Ibrahim Yakubu Addis, a Facebook.
Wadanda da aka kama sun hada da Murtala Garba Doka da Shamsu Safiyanu Lambu wanda aka fi sani da Shamzeet Lambu.
Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwaRahotanni sun bayyana cewar shugaban karamar hukumar ne ya bayar da umarnin kama su ne a ranar Litinin.
Shamzeet Lambu ya wallafa a Facebook, inda ya zargi shugaban karamar hukumar da kin kammala aikin titin Lambu zuwa Banki zuwa Yarimawa da Jakata, wanda gwamnatin jiha ta amince da shi kan kudi kimanin naira miliyan 240.
A rubutun da ya wallafa cikin harshen Hausa, Lambu ya ce: “Naira miliyan 240 kudinmu a Burji, Allah Ya saka mana.”
Rahotanni sun nuna cewa an fara tsare mutanen biyu a ofishin ’yan sanda na Tofa, kafin daga bisani aka mayar da su hedikwatar rundunar da ke kwaryar birnin Kano a Bompai domin ci gaba da bincike.
Shugaban matasa na yankin, Kwamared Nazifi Ado Lambu, ya tabbatar da kamen, inda ya ce hakan ya tayar da hankalin jama’a a yankin.
“E, an kama su saboda rubutun da suka yi a Facebook game da aikin titi. An tsare su a Tofa kafin daga bisani aka kai su Bompai,” in ji shi.
Wani mazaunin Lambu, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce al’ummar yankin sun dade suna rokon shugaban karamar hukumar kan gyara titin.
“Ya taba yin alkawarin zai gina titin da bututun ruwa da kwalta, amma bayan gwamnatin jiha ta amince da aikin, sai aka tsaya a iya share titi da zuba yashi, sai kuma aka bar aikin,” in ji mazaunin.
Da aka tuntubi shugaban karamar hukumar, Ibrahim Yakubu Addis, ya ce shi ne ya kai kara ofishin binciken laifuka (CID) domin a tabbatar da gaskiyar zargin da ake yi masa.
“Ba mu yi musu komai ba illa tambayarsu su kawo hujjar zargin da suka yi. Mutane da yawa suna ganin abin da ake wallafawa a intanet, kuma ba wannan ne karo na farko da suke irin wannan ba,” in ji shi.
Ya kuma ce adadin kudin aikin da suke zargi ba gaskiya ba ne.
“Gwamna ya amince da aikin da kudi kasa da Naira miliyan 100, ba miliyan 240 ba.
“Mun dai ce su kawo hujja kawai,” in ji shugaban.
Kamen mutanen biyu ya haifar da ce-ce-ku-ce a Karamar Hukumar Tofa, inda jama’a ke kira da a warware lamarin cikin lumana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Karamar Hukuma zargi shugaban karamar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Mataimakin Shugaban Amurka Dick Cheney ya mutu
Tsohon Mataimakin Shugaban Amurka, Dick Cheney, ya rasu yana da shekaru 84 a duniya.
Cheney shi ne mataimakin shugaban ƙasa na 46, wanda ya yi aiki tare da tsohon shugaban ƙasa, George W. Bush a wa’adin mulki biyu daga shekarar 2001 zuwa 2009.
An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a MaiduguriA cewar iyalansa, marigayin ya rasu bayan doguwar jinyar da ya yi fama da ita sakamakon ciwon huhu da na zuciya da jijiyoyin jini.
Dick Cheney, wanda aka san shi da tsananin ra’ayin mazan jiya, yana daga cikin mataimakan shugabanni mafi tasiri a tarihin Amurka.
Ya taka muhimmiyar rawa wajen yaƙin Iraki, tare da goyon bayan amfani da na’urorin leƙen asiri da bincike mai tsanani a matsayin martani ga harin ta’addanci na ranar 11 ga Satumba, 2001.
Bayan ya bar ofis, Cheney ya zama ɗaya daga cikin masu sukar salon jagorancin shugaban ƙasa Donald Trump a wa’adin mulkinsa na farko, musamman bayan ’yarsa, Liz Cheney, ta zama jigo cikin ’yan jam’iyyar Republican da suka fito fili suna sukar Trump, lamarin da ya zamo sila dakatar da shi daga jam’iyyar.
Liz Cheney ta kasance ɗaya daga cikin ’yan jam’iyyar da suka soki matakin magoya bayan Trump na tayar da tarzoma a ginin Majalisar Dokoki ta ƙasar (Capitol) bayan shan kaye a zaɓen ranar 6 ga Janairu, 2021.