Aminiya:
2025-11-07@17:56:26 GMT

An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai

Published: 7th, November 2025 GMT

Al’ummar Ƙauyen Sarai da ke Ƙaramar hukumar Dawakin Kudu a Jihar Kano sun shiga ruɗani a ranar Alhamis bayan da aka gano gawar wata mata mai shekara 96 ​​a cikin  masai.

Jami’in hulɗa da jama’a na Hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya bayyanawa manema labarai a ranar Juma’a.

Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800

Abdullahi ya ce, sashin bayar da agajin gaggawa na hukumar ya samu kiran gaggawa daga wani mai suna Usman Adamu ranar Alhamis, inda ya bayyana cewa wata tsohuwa ta faɗa cikin masai a ƙauyen Sarai.

“Hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Daraktan, Sani Anas ta samu kiran gaggawa daga Usman Adamu da misalin ƙarfe 9:27 na safiyar ranar Alhamis, 6 ga watan Nuwamba, 2025, inda ya bayar da rahoton ibtila’in da wata mata ta faɗa cikin ramin masai a ƙauyen Sarai da ke ƙaramar hukumar Dawakin Kudu,” a cikin sanarwar.

“Jami’anmu na sashen agajin gaggawa daga hedikwatar hukumar ta isa wurin, inda ta gano wata mata mai suna Habiba Ado mai shekara 96, wanda ’yan uwanta suka ce tana fama da taɓin hankali,” in ji shi.

Abdullahi ya bayyana cewa, ‘yan uwanta ​​sun shafe kwanaki huɗu suna nemanta kafin a gano gawarta a cikin masai ranar Alhamis.

“Sun kuma yi kira ga mai gidan da ya rufe ramin masan don hana afkuwar irin haka nan gaba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa jami’an ceto sun gano  matar daga cikin ramin, amma an tabbatar da mutuwar ta.

Tuni dai aka miƙa gawarta ga Hakimin Unguwa, Alhaji Musa Muhammad domin yi mata jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dawakin Kudu a Jihar Kano ranar Alhamis

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Dakta Bukar ya bayyana wannan hadin gwiwar a matsayin abu mai muhimmanci wanda yazo a kan gaba wajen karfafa wayar da kan jama’a game da rawar da sahihan bayanai suke takawa wajen tsara ci gaba da samar da manufofi masu tushe , da dorewar cigaban kasa.

 

Dakta Bukar, ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa da kafafen yada labarai wajen isar da bayanan Hukumar ga al’umma.

 

A cikin jawabinsa, Kwamishinan yada labarai Malam Ahmed Maiyaki, ya yaba da wannan shiri tare da tabbatar da cikakken goyon bayan Ma’aikatarsa ga manufofin Hukumar.

 

Yace samar da sahihan da kafa gwamnati mai wacce da dogara da adalci yana daga cikin manifofi da kudirorin gwamnatin jihar Kaduna wanda hakan zai taiama wajen kawo ci gaba ga al’umma baki daya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai ‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara November 4, 2025 Labarai Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU November 4, 2025 Labarai 2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC November 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka
  • Matan 500 Za Su Amfana da Gwajin Cutuka Kyauta a Jihar Gombe
  • ‘YanSandan Jihar Kwara Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su
  • Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma
  • HOTUNA: Mun kori jami’ai fiye da 100 cikin shekara guda — DSS
  • Barazanar Trump: Ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Nijeriya — Tuggar