HausaTv:
2025-11-06@09:51:23 GMT

Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho

Published: 6th, November 2025 GMT

Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya bukaci Amurka da Turai su nuna gaskiya idan suna son sake gina aminci da Iran.

A wata tattaunawa ta wayar tarho tsakanin Shugaba Emmanuel Macron na Faransa,  da takwaransa na Iran Mas’ud Pezeshkian, shugaban na Iran ya ce dole ne turai su mutunta ‘yancin Iran kuma su daina gabtar da bukatu da Iran ba za ta taba amincewa da su ba.

Iran ta yi maraba da tattaunawa amma Pezeshkian ya sake nanata cewa, a yanzu ba Iran ce za ta tabbatar da gaskyarta ba, domin ta riga ta yi haka, ya rage kan kasashen turai ne su tabbatar wa duniya cewa da gaske suke yi a cikin abin da suke furtawa.

Duk da haka, ya ce, Iran na ci gaba da fuskantar zarge-zarge marasa tushe da kuma ƙarin takunkumi a ƙarƙashin hujjar cewa tana hankoron kera mkaman nukiliya.

Pezeshkian ya jaddada cewa za a iya magance matsaloli ne kawai ta hanyar tattaunawa  da mutunta juna, ba ta hanyar tilastawa ko barazana ba.

“Inda za a iya magance rashin fahimta ta hanyar yin amfani da hankali, me ya kawo maganar yin amfani a karfi da kashe-kashe da rusa gine-gine da ababen mor rayuwa na al’ummar kasa.

A nasa bangaren, Macron ya gode wa Pezeshkian saboda matakan da aka dauka don aiwatar da yarjejeniyoyin da suka gabata kuma ya bayyana niyyarsa ta yin aiki don samar da sabon tsari na tattaunawa tsakanin Iran da kasashen Yammacin duniya.

Ya ce ci gaba da tattaunawa yana da mahimmanci don gina gaskiya da aminci, da dage takunkumi, da kuma inganta dangantakar kasashen biyu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya Ta Sake Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar November 6, 2025 Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya November 6, 2025 Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba November 6, 2025 Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya November 6, 2025 An Kama ‘Yan Jarida 3 A Nijar Bisa Tuhumar  Fitar Da Bayanai Na Hukuma November 5, 2025 Sudan Ta Sake Jaddada Tuhumar Kasar UAE  Da Taimakon Rundunar RSF November 5, 2025 Shugaban Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin  Jihadi Suke Yi November 5, 2025 Iran : bisa sharadi ne muka saki ‘yan Faransa daga gidan yari November 5, 2025 Gaza : MDD Ta damu kan keta yarjejeniya tsagaita wuta da Isra’ila ke yi  November 5, 2025 Kungiyoyin agaji sun ce tallafin da ake bai wa Gaza bai isa ba November 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, ta ce wasu shugabannin kasashen waje za su hallara a birnin Shanghai, domin halartar baje kolin hajojin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE karo na takwas, wanda zai gudana tsakanin ranakun 5 zuwa 10 ga watan nan na Nuwamba.

 

Kakakin wadda ta bayyana hakan a Litinin din nan, ta ce cikin shugabannin da ake sa ran za su halarci bikin bude baje kolin na CIIE, da sauran ayyuka masu nasaba da shi bisa gayyatar da aka yi musu, akwai firaministan kasar Georgia Irakli Kobakhidze, da na Serbia Djuro Macut, da kakakin majalisar wakilan tarayyar Najeriya Abbas Tajudeen, da shugaban majalisar gudanarwar kasar Slovenia Marko Lotric. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka November 3, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan November 3, 2025 Daga Birnin Sin Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya
  • Iran : bisa sharadi ne muka saki ‘yan Faransa daga gidan yari
  • Khatibzadeh: Shirin Nukiliya na Iran ya fi bayyana a duniya
  •  Ansarullah: Dakarunsu A Shirye Suke Don Tunkarar Duk Wata Barazana Daga Isra’ila
  • Kakakin Dakarun IRGC Ya Ce; Ko Kadan Amurka Ba Abar Amincewa Ba Ce
  • Admiral Sayyari Ya Ce: Isra’ila Ba Ta Kai Matsayin Da Zata Yaki Iran Ba
  • Iran : Jagora ya gindaya wasu sharudda kafin yin duk wata hulda da Amurka   
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yayi Maraba Da Kalaman Da Hukumar IAEA Ta yi Kan Shirin Nukuliyarta
  • Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai