Aminiya:
2025-11-07@22:23:50 GMT

Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi a Aso Rock

Published: 8th, November 2025 GMT

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya gana da Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Juma’a.

Sarkin Musulmi, wanda shi ne Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), ya gana da Shugaban Ƙasa ba tare da ’yan jarida ba.

Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu — Tinubu Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800

Ganawar na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan Shugaba Tinubu ya gana da Archbishop Ignatius Kaigama na Katolikan Abuja, a wani yunƙuri na inganta dangantakar addinai da zaman lafiya a Najeriya.

Ko da yake ba a bayyana abin da suka tattauna ba, amma ganawar ba za ta rasa nasaba da ƙarfafa fahimtar juna tsakanin addinai da kuma bunƙasa haɗin kan ƙasa da ci gaba.

Hakan na zuwa ne bayan shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya bisa zargin cin zarafin Kiristoci.

Bayan ganawar, Sarkin Musulmi, ya raka Shugaba Tinubu zuwa sallar Juma’a a Masallacin Fadar Shugaban Ƙasa.

A lokacin huɗubar sallar Juma’ar, limamin masallacin, Alhaji Abdulwaheed Abubakar, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su tallafa wa ƙoƙarin gwamnati na ƙarfafa zaman lafiya da tsaro.

Ya tunatar da jama’a cewa zaman lafiya shi ne ginshiƙin ci gaban al’umma da ci gaban ƙasa baki ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ganawa Sarkin Musulmi Zaman lafiya Shugaban Ƙasa Sarkin Musulmi

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

Akpabio ya mayar da martani cewa ba su da niyyar ɓata lokaci, inda ya ce, “Ba zan jira kowa ba, saboda da zarar an tantance su, ba za a sake ganinsu ba.”

Daga nan sai ‘yan majalisar suka shiga zaman sirri domin tattauna batutuwan da suka shafi ƙasa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu  November 5, 2025 Manyan Labarai ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya November 5, 2025 Da ɗumi-ɗuminsa Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86 November 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • GORON JUMA’A
  • Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar
  • An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8
  • Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro
  • Likitoci sun wayar da kan mata kan cutar Sankara a Gombe
  • Kwamishinan Kano Na Ziyarar Tabbatar Da Zaman Lafiya A Wannan Kaka
  • An yi musayar yawu tsakanin Barau da Akpabio a majalisa kan barazanar Trump