Aminiya:
2025-11-10@08:19:22 GMT

An sake rage kuɗin aikin Hajjin 2026 a Najeriya

Published: 10th, November 2025 GMT

An ƙara rage kuɗin kujerar aikin hajjin bana zuwa aƙalla Naira miliyan 7.5 ga maniyyata daga jihohin Arewacin Nijeriya.

Shugaban Hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan ne ya bayyana haka a wata tattaunawa da manema labarai.

Ya ce an rage kuɗin ne sakamakon umarnin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na yin hakan da kuma tattaunawar da suka yi ta baya-bayan nan da kamfanonin Saudiyya.

A ƙarƙashin sabon farashin yanzu jihohin da ke shiyyar Borno/Adamawa za su biya Naira 7,579,0202 maimakon Naira 8,327,125 da hukumar ta sanar a baya.

Mahaifiyar Minista Balarabe Lawal Abas ta rasu NAJERIYA A YAU: Dalilan Yaɗuwar Cututtuka A Irin Wannan Lokaci

Sauran jihohin Arewa kuma sabon farashinsu shi ne Naira 7,669,769 maimakon Naira 8,457,685 da aka sanar da farko.

Jihohin Kudancin Nijeriya kuwa za su biya Naira 7,991,141 saɓanin Naira 8,784,085.

Sai dai yanzu an kayyade ranar 05 ga watan Disamba ta zama wa’adin ƙarshe da duk maniyyatan Nijeriya za su cika kuɗin kujerarsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: maniyyata Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

3. A Hangen Nesansa wajen jagorancin al’umma, ya mayar da hankali kan masana’antu, sabunta ababen more rayuwa da kuma gina Dan’adam; domin mayar da Jihar Nasarawa matsayin wata babbar cibiyar zuba jari a Nijeriya da horar da aikin injiniya tare da kyautata jin dadin al’ummar jihar; an zabi Injiniya Abdullahi A. Sule a matsayin Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025.

Injiniya Abdullahi Sule: Wanda Ya Fi Yin Fice Kan Harkokin Masana’antu A Duk Fadin Arewa

4. Shugabancinsa ya yi matukar kawo sauye-sauye a Jihar Ekiti, musamman ta hanyar gudanar da mulki na adalci, sabunta ayyukan more rayuwa, karfafa matasa da fadada aikin gona; sakamakon tawali’un da yake da shi da horon da ya samu wajen tafiyar harkokin kudi da gina jama’a tare kuma karfafa al’adun demokuradiyya; ya sa aka zabi Biodun Abayomi Oyebanji a matsayin Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025.

Biodun Abayomi Oyebanji: Wanda Ya Kawo Juyin-juya-hali A Jihar Ekiti

5. A sauyin da ya kawo a shugabancinsa, jajircewarsa na kawo ci gaba a fannin tsaro, zuba jari mai yawan gaske a fannin ilimi, kiwon lafiya da sauran ababen more rayuwa; kazalika a kokarinsa na sake mayar da Jihar Zamfara kan turbar zaman lafiya da ci gaba mai dorewa, Dauda Lawal shi ne Gwarzon Gwamnanmu na wannan shekara.

Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

6. Ya dukufa wajen mayar da hankali kan manufar da ya sanya gaba, mai taken; “MORE Agenda”, wanda ya sake fasalin tsarin mulkin Jihar Delta ta hanyar zaman lafiya, hadin kai da kuma jajircewa wajen samar da ababen more rayuwa, ilimi, lafiya da kuma gina al’adun jama’a bisa gaskiya, tsantseni a sha’anin harkar kudi ta bangarori da dama; Rt. Hon. Sheriff Oborebwori, shi ne gwarzon gwamnanmu na 2025.

Sheriff Oborebwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

7. Saboda kasancewarsa mai sasanta mutane da hada kansu duk da bambance- bambancensu; ga kuma samar da abubuwan more rayuwa a kauyuka, farfado da lamarin kula da lafiyar al’umma, taimaka wa manoma da matasa yadda za su tsaya da kafafunsu; tafiyar da gwamnati ta tausaya wa al’umma, yin biyayya da dokoki, da tunanin yadda gaba za ta yi kyau; shi ya sa aka zabi Sanata Uba Sani a matsayin Gwarzon Gwamnan shekarar 2025.

Sanata Uba Sani: Mai Hada Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

Gwarzon Dan Majalisa Na Shekarar 2025

8. Saboda yadda ya shahara wajen yin doka, wakilci, nuna damuwa da sai abu ya kasance; yadda yake da hazaka, sa ido kan ci gaban inda yake wakilta, da kokarin samar da zaman lafiya, tsarin da ya sa aka samu cimma buri a gyaran tsarin mulki, hadin kan kasa;. Honorabul Benjamin Okezie Kalu, PhD, CFR don haka shi ne dan majalisar shekarar 2025.

Benjamin Okezie Kalu: Wakili A Majalisa Saboda Hadin Kan Kasa, Zaman Lafiya, Da Ci Gaba

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025

9. Bisa la’akari da yadda ya tafiyar da sha’anin kawo gyara a lamarin tara haraji, abin da aka aiwatar ta yadda ya dace a yi da gaskiya domin habbaka hanyoyin samun kudaden shiga ba ta hanyar man fetur ba, amma ta hanyar bullo da wasu dabaru ta kafar sadarwa ta zamani; da yake an dauki hukumomin gwamnati da su ma abokan tafiya ne domin samun ci gaba, ba tare da an sa wani abu na matsi ba; Dakta Zacch Adedeji a yanzu shi ne gwarzon ma’aikakaci na shekarar 2025.

Dakta Zacch Adedeji: Wanda Ya Kara Daukaka Darajar Haraji A Nijeriya

Gwarzon Dan Kasuwa Na 2025

10. Saboda hangen nesansa wajen kawo gyara a lamarin bunkasa samar da takin zamani a Nijeriya da kuma harkar kasuwancin amfanin gona; don tallafa wa miliyoyin manoma hanyar amfani da abubuwan gida. Da kuma kokarinsa na samar da wata hanyar taimakawa masu karamin karfi yadda za su cimma burinsu na maida aikin gona a matsayin wata hanya da za ta taimaka wa al’umma; don haka Thomas Etuh shi ne gwarzon Dan kasuwa na shekarar 2025.

Thomas Etuh: Gwarzo Wajen Samar Da Hanyoyin Dogaro Da Kai Ga Matasa

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025

11. Domin jagorantar bangaren hakar mai da iskar gas na tekun Nijeriya da ya yi nasarar samar da ganga miliyan 1.8 na man fetur a kowace rana; da kuma jagorantar hukumar NUPRC ta zarce burinta na samun kudaden shiga da kashi 84.2 cikin dari, Injiniya Gbenga Komolafe shi ne Gwarzon Shugaban Kamfani na Shekara ta 2025.

Gbenga Olu Komolafe: Jagorantar Tsarin Samar Da Makamashi A Nijeriya

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025

12. Domin jagorantar harkar kudi ta hanyar kirkire-kirkire tare da karfafa samar da kanana da matsakaitan sana’o’i (MSME) 700,000 da karfafa tubalin tattalin arzikin Nijeriya da kuma sake fasalta banki; an zabi Dakta Tony Okpanachi a matsayin Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025.

Dr Tony Okpanachi: Gina Makomar Nijeriya Ta Hanyar Tallafa Wa Kananan Kamfanoni

Wanda Da Ya Fi Tasiri A Kafofin Sada Zumunta Na Shekarar 2025

13. Domin sauya rikici zuwa hadin kai, da tashin hankali zuwa ci gaba mai ma’ana da kirkirar ayyukan yi, samar da zaman lafiya da sabunta zamantakewa, al’adu da tattalin arzikin Neja Delta da zuba jari a ilimi, kiwon lafiya, muhalli da karfafa ci gaba, an zabi Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo) a matsayin mafi tasiri a Kafofin Sada Zumunta na 2025.

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

Gwarzuwar Hukumar Gwamnati Ta Shekarar 2025

14. Domin fadada iyakokin aiwatar da doka a Nijeriya tare da dawo da fiye da naira biliyan 10 ga masu amfani da kayayyaki tare da kalubalantar rashin adalci na kamfanoni da kafa sabbin ka’idoji kula da kasuwanci ta kafafen sadarwar zamani da tabbatar da adalci da shugabanci na na gari — Hukumar Kare ‘Yancin Masu Amfani da Kayayyaki ta Kasa (FCCPC), ita ce Gwarzuwar Hukumar Gwamnati ta Shekarar 2025.

Hukumar Kare ‘Yancin Masu Amfani Da Kaya (Fccpc): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

SkalesShi Ne Gwarzon Mawakin Shekarar 2025

15. Sakamakon tasirin da ya dade yana yi a fannin waka a Nijeriya da kasashen waje. Shahararriyar wakarsa “Shake Body”, wacce ta kai ga samun miliyoyin masu sauraro a Spotify da kuma kwarewarsa a fannin fasahar hada al’umma daban-daban. SKALES ne Gwarzon Mawakin Shekarar 2025.

Kanyenyachukwu Tagbo Okeke Shi Ne Gwarzon Mai Zane Na Shekarar 2025

16. Saboda sanya Nijeriya a taswira ta duniya tare da Guinness World Record (GWR) na Mafi Girman Zanen Canbas da mutum daya ya yi a wannan shekara, da kuma wayar da kan jama’a kan cutar autism a Nijerriya, tare da amfani da fasaha wajen karfafa hadin kai da ilimi ga mutane masu kwarewa daban-daban, Kanyenyachukwu (wanda aka fi sani da Kanye) Tagbo-Okeke shi ne Gwarzon Mai Zane na Shekara 2025.

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025

17. Saboda jagorantar Super Falcons zuwa nasarar lashe kofin WAFCON karo na 10, wanda ya kara musu tasiri; da nuna kwarewa a dabaru da shugabanci da dawo da aminci a kwallon kafar Nijeriya da kuma karfafa sabon karni na masu horar da kwallo a Afirka, Justine Madugu shi ne gwarzon mai koyar da wasanni na Shekarar 2025.

Justine Madugu: Mai Dabaru Dawo Da Darajar Kwallon Kafa A Nijeriya

Dabid Adeyemi Shi Ne Gwarzon Matashi Na Shekara 2025

18. Dangane da habaka kirkira, tausayi da kwarewa ta hanyar kirkirar manhajar AI wacce ke sauya yadda dalibai masu nakasar gani ke samun ilimi a Nijeriya da wajenta, Dabid Adeyemi shi ne Gwarzon Matashi na Shekarar 2025.

Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025

19. Domin ganin yadda ya sauya akalar samar da kiwon lafiya cikin tausayi da soyayya ga mabukata tare da yi wa mutane fiye 2,600 tiyata kyauta a sassan kasar nan. Dr Seidu Adebayo Bello shi ne Gwarzon Ma’aikacin Kiwon Lafiya na shekarar 2025.

Dr Seidu Adebayo Bello: Ya Dawo Da Fata Ga Al’umma

Misis Mabel Ijeoma Duaka Shi Ne Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025

20. Duk da ayyukan ta’addanci na Boko Haram, yayin da al’umma musamman baki ke gudu daga yankuna da dama na Jihar Borno, ta gwammace ta zauna a karamar hukumar Mafa domin ci gaba da bayar da kulawa ga wadanda suka jikkata na tsawon shekara 21. Mrs Mabel Ijeoma Duaka ce Gwarzuwar Ma’akaciyar jinya ta shekarar 2025

Bankin Probidus Ne Gwarzon Banki Na Shekarar 2025

21. Saboda kasancewa kan gaba wajen zamanantar da harkokin Banki a Nijeriya da kuma karfafa wa manya da kananan masa’na’antu tare da zama a kan gaba wajen daukaka darajar aikin Banki a Nijeriya, Bankin Probidus ne Gwarzon bankinmu na shekarar 2025.

Gwarzuwar Matashiya ‘Yar Makaranta Ta Shekarar 2025

22. Domin nasarar da ta samu wajen sanya sunan Nijeriya a fagen ilimi a duniya da jajircewa, hazaka da bayar da shawarwari don zaburar da sabbin dalibai don rungumar harshe Turanci da tabbatar da nasara na iya tasowa daga kowane bangare. An bai wa Nafisa Abdullahi Aminu lambar yabo ta Gwarzuwar Matashiyar 2025.

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Daukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Hukumar NASENI Ne Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025

23. Domin yadda ta jagoranci ci gaban masana’antu, samar da makamashi, da fasahohin da suka dace da yanayin da ke rage fitar da iskar carbon mai guba da inganta hanyoyin samar da wutar lantarki mai tsabta; karfafa masu kirkire-kirkire na cikin gida, samar da dabarun tattalin arzikin mai dorewa, da habaka dogaro da kai a Nijeriya ta hanyar bincike da kula da muhalli, Hukumar NASENI ce Gwarzuwar Hukumar da ta fi tasiri wajen kare muhalli a shekarar 2025.

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kudade Na Shekarar 2025

24. Don kawo sauyi a harkokin kudade ta hanyar fasahar zamani da suka hada da kirkira da gaskiya wajen karfafa miliyoyin ‘yan Nijeriya, kanana da matsakaitan kamfanoni (MSME) ta hanyar amfani da wayar hannu, don kawo karshen matsalolin kudade ta hanyar fasahar zamani, OPay Nigeria ya amsa sunansa na zama gwarzon kamfanin fasahar harkokin kudade na shekarar 2025.

OPay Nigeria: Tabbatar Da ‘Yancin Hada-hadar Kudi

Kamfanin GEIL: Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025

25. Domin jagorantar bunkasawa da gudanar da tashar fitar mai na farko a Nijeriya fiye da shekaru 50, Kamfanin GEIL shi ne Gwarzon Shekarar 2025

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025

26. Domin habaka samar da ruwan sha mai inganci da arha, dandano da wayar da kan ‘yan kasa kan amfani da tsaftataccen ruwa, kamfanin Nestlé Pure Life Nigeria Plc shi ne gwarzon samar da kaya a shekarar 2025.

Kamfanin Nestlé Pure Life: Tsarinsa Da Manufa

Kamfanin Trade Modernisation Project: Gwarzon Kamfani Na Shekarar 2025

27. Domin sauya tsarin kasuwancin Nijeriya ta hanyar fasahar zamani da inganci, sarrafa ayyuka, kara habaka samun kudaden shiga da saukaka gudanar da kasuwanci, bunkasa hadin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu, samar da ayyukan yi da karfafa gasa, Kamfanin Trade Mo

dernisation Project (TMP) shi ne gwarzon Kamfanin shekarar 2025.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Rahotonni Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya October 17, 2025 Rahotonni Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya October 11, 2025 Rahotonni Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL
  • Minista Goronyo ya Duba Ci Gaban Aikin Titin Abuja Zuwa Kano
  • Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala
  • Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar Najeriya
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu!
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026