Majalisar Zartarwar Jihar Jigawa ta amince da wasu manyan kwangiloli da kudinsu ya haura Naira Biliyan 6, domin karfafa bangarorin noma, ilimi da ci gaban tattalin arziki a fadin jihar.

A cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai bayan zaman majalisar da aka gudanar a fadar gwamnatin Dutse, kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya bayyana cewa wannan mataki na nuna kudirin gwamnatin jihar wajen inganta muhimman bangarori da ke da tasiri kai tsaye ga rayuwar al’umma.

A cewarsa, majalisar ta amince da kashe sama da Naira biliyan 2 domin sayen babura nau’in Hunter guda 1,180 ga malaman gona a fadin jihar.

Ya ce wannan mataki ya yi daidai da kokarin Gwamna Umar Namadi na bunkasa harkar noma da raya karkara. Baburan za su taimaka wajen saukaka zirga-zirgar malaman gonan domin su rika koyar da manoma sabbin hanyoyin noma da za su taimaka wajen samun karin amfanin gona.

Haka kuma, majalisar ta amince da kashe sama da Naira biliyan 2 da miliyan 300 domin gina sabbin kasuwanni na zamani a Maigatari, Shuwarin da Hadejia.

Kwamishinan ya bayyana cewa, wannan shiri na da nufin karfafa hanyoyin samun kudaden shiga na cikin gida da samar da yanayi mai kyau don kasuwanci da ciniki.

Alhaji Sagir ya kara da cewa, majalisar ta kuma amince da fitar da sama da Naira Biliyan 1 domin gina katanga a makarantun gwamnati 15 a fadin jihar, domin kare rayuka da dukiyoyin dalibai da malamai tare da inganta yanayin karatu.

Bugu da kari, majalisar ta amince da kwangilar sama da Naira Biliyan 1 da miliyan 300 domin sayen injinan nika shinkafa na zamani guda 200, da kayan aikin walda, da na kera kayayyaki da kayan yin fenti, don cibiyar koyon sana’o’i ta zamani da aka kammala ginawa a Limawa, karamar hukumar Dutse.

Ya ce wannan mataki zai taimaka wajen hanzarta kokarin gwamnatin jihar na samar da ayyukan yi ga matasa marasa aikin yi da kuma karfafa sana’o’in dogaro da kai.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa KASUWANCI sama da Naira Biliyan majalisar ta

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

Mai bai wa Gwamnan Filato shawara kan harkar tsaro, Janar Shippi Goshwe (mai ritaya), ya tabbatar da cewa gwamnati tana ɗaukar sabbin ma’aikata ƙarƙashin Operation Rainbow domin inganta tsaron al’umma.

Shugaban Ƙungiyar Matasan Berom (BYM), Barista Solomon Nwantiri, ya yi Allah-wadai da kisan tare da tambayar dalilin da ya sa ake amfani da zargin satar shanu a matsayin hujjar kashe mutanen da ba su ji ba su gani ba.

Waɗannan hare-haren sun ƙara jaddada buƙatar ɗaukar matakin gaggawa da adalci domin kawo ƙarshen kashe-kashe a ƙauyukan Jihar Filato.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson October 16, 2025 Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02% October 15, 2025 Manyan Labarai 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NIEPA Ta Jinjinawa UNICEF Bisa Kare Hakkokin Yara Na Samun Ilimi A Najeriya
  • Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata
  • Jihar Jigawa Ta Dukufa Wajen Gina Magudanan Ruwa Domin Kaucewa Ambaliya
  • Saudiyya ta zaftare wa Najeriya guraban Aikin Hajji da sama da kujeru 28,000
  • Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafin Kayayyakin Sana’o’i A Karamar Hukumar Gagarawa
  • An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato
  • Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa