Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 6 Don Bunkasa Noma, Ilimi Da Kasuwanci
Published: 17th, October 2025 GMT
Majalisar Zartarwar Jihar Jigawa ta amince da wasu manyan kwangiloli da kudinsu ya haura Naira Biliyan 6, domin karfafa bangarorin noma, ilimi da ci gaban tattalin arziki a fadin jihar.
A cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai bayan zaman majalisar da aka gudanar a fadar gwamnatin Dutse, kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya bayyana cewa wannan mataki na nuna kudirin gwamnatin jihar wajen inganta muhimman bangarori da ke da tasiri kai tsaye ga rayuwar al’umma.
A cewarsa, majalisar ta amince da kashe sama da Naira biliyan 2 domin sayen babura nau’in Hunter guda 1,180 ga malaman gona a fadin jihar.
Ya ce wannan mataki ya yi daidai da kokarin Gwamna Umar Namadi na bunkasa harkar noma da raya karkara. Baburan za su taimaka wajen saukaka zirga-zirgar malaman gonan domin su rika koyar da manoma sabbin hanyoyin noma da za su taimaka wajen samun karin amfanin gona.
Haka kuma, majalisar ta amince da kashe sama da Naira biliyan 2 da miliyan 300 domin gina sabbin kasuwanni na zamani a Maigatari, Shuwarin da Hadejia.
Kwamishinan ya bayyana cewa, wannan shiri na da nufin karfafa hanyoyin samun kudaden shiga na cikin gida da samar da yanayi mai kyau don kasuwanci da ciniki.
Alhaji Sagir ya kara da cewa, majalisar ta kuma amince da fitar da sama da Naira Biliyan 1 domin gina katanga a makarantun gwamnati 15 a fadin jihar, domin kare rayuka da dukiyoyin dalibai da malamai tare da inganta yanayin karatu.
Bugu da kari, majalisar ta amince da kwangilar sama da Naira Biliyan 1 da miliyan 300 domin sayen injinan nika shinkafa na zamani guda 200, da kayan aikin walda, da na kera kayayyaki da kayan yin fenti, don cibiyar koyon sana’o’i ta zamani da aka kammala ginawa a Limawa, karamar hukumar Dutse.
Ya ce wannan mataki zai taimaka wajen hanzarta kokarin gwamnatin jihar na samar da ayyukan yi ga matasa marasa aikin yi da kuma karfafa sana’o’in dogaro da kai.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa KASUWANCI sama da Naira Biliyan majalisar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran.
A wani bangare na huldar duplomasiya tsakanin iran da saudiya , mataimakin ministan harkokin wajen kasar saudiya Saud bin mohammad Al-sati ya gana da ministan harkokin wajen kasar iran Abbas Araqchi a nan birnin tehran inda suka tattauna kan batutuwan da suka shafin alakokin dake tsakani da kuma ci gaban yankin.
Ganawar wani bangare ne na kokarin da kasashen biyu ke yi na kara karfafa dangantakar dake tsakaninsu da kuma ci gaba da tattaunawa kan batutuwa masu tsauri, saudiya da iran sun kara fifita huldar diplomasiya domin shawo kan rikicin da ake ciki a yankin da kuma samar da damarmakin yin aiki tare.
Ganawar tasu ta zo ne adaidai lokacin da ake cikin mawuyacin halin a yankin da suka hada da yankin falasdinu, labanon da kuma kasar siriya, dukkan kasashen suna taka muhimmiyar rawa a lamurran da suka shafi yankin, tattaunawa ta kai tsaye itace mafita na rage matsalolin da kuma bayyana damuwarsu.
Ana sa bangaren Saud bin mohammad Sati mataimakin ministan harkokin wajen saudiya ya jaddada muhimman kara karfafa alaka da kuma yin aiki tare domin fuskantar kalubalen tsaro da yankin ke ciki.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Lebanon: Sakon Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma December 1, 2025 Ireland Ta Sauya Sunan Wurin Shakatawa Daga Na Shugaban “Isra’ila” Zuwa Na Shahidiyar Falasdinu November 30, 2025 Gaza: Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki November 30, 2025 Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala November 30, 2025 MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari November 30, 2025 An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Turkiya November 30, 2025 An yi gangami a fadin duniya a zagayowar ranar Falasdinu November 30, 2025 Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5 November 30, 2025 Najeriya : Sojoji sun kubutar da yan mata 12 da mayakan ISWAP November 30, 2025 An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci