A yau Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada bukatar gina ingantaccen yankin ciniki cikin ’yanci na tashar ruwa ta Hainan ko FTP a takaice. Shugaba Xi ya bayyana bukatar ne yayin dake sauraron rahoton aiki game gina yankin na FTP a birnin Sanya na lardin Hainan dake kudancin kasar Sin.

A cewarsa, gina yankin FTP na Hainan muhimmiyar manufa ce ta kwamitin kolin JKS, wadda aka tsara domin zurfafa cikakkun sauye-sauye, da bude kofa ga waje a sabon zamani.

Shugaban na Sin ya kara jaddada bukatar kyautata nazari, da aiwatar da ka’idojin aiki na cikakken zama karo na hudu na kwamitin kolin JKS na 20, tare da kokarin cimma burikan da aka sanya gaba, dangane da bunkasa yankin FTP na Hainan a dukkanin fannoni, ta hanyar lura da tsare-tsare, da aiki tukuru da wanzar da kwazon aiki.

A ranar 18 ga watan Disamban bana ne yankin FTP na Hainan, zai kaddamar da ayyukan kwastam na musamman na daukacin tsibirin, matakin da shugaba Xi ya ce zai kasance jigon matakai da kasar Sin za ta aiwatar, don fadada bude kofa mai inganci, da ingiza gina budadden tattalin arzikin duniya. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu November 6, 2025 Daga Birnin Sin Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki November 5, 2025 Daga Birnin Sin Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka November 5, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, ta sanar a yau Litinin cewa, bisa gayyatar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi masa, sarkin Spaniya Felipe VI, zai gudanar da ziyarar aiki a kasar Sin, daga ranar 10 zuwa 13 ga watan nan na Nuwamba. (Mai fassara Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce November 3, 2025 Daga Birnin Sin An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau November 3, 2025 Daga Birnin Sin Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai November 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
  • Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
  • Jirgin ƙasa ya murƙushe babur mai ƙafa uku a Jos
  • ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gina Gadar Sama Da Ta Kasa A Mararraba
  • HOTUNA: Mun kori jami’ai fiye da 100 cikin shekara guda — DSS
  • KADUNA TA ZAMA JIHAR FARKO A NIJERIYA DA TA AIWATAR DA SHIRIN SAMAR DA ABINCIN MAI GINA JIKI GA YARA – UNICEF
  • Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin