Leadership News Hausa:
2025-11-09@21:47:28 GMT

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Published: 9th, November 2025 GMT

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugabar kwamitin wasannin Olympics na duniya (IOC) Kirsty Coventry da kuma shugaban kwamitin na karramawa Thomas Bach a Guangzhou, babban birnin lardin Guangdong da ke kudancin kasar Sin.

Xi ya nuna cewa, kasar Sin ta kasance mai himma, mai ba da kariya kuma mai yayata ruhin wasannin Olympics.

Ya ce, gasar wasanni ta kasa ita ce babban bikin wasanni mafi girma a kasar Sin. Kuma yankunan Guangdong, Hong Kong da Macao ne suka hada hannu wajen shirya gasar wasannin ta kasa karo na 15. Ana kyautata zaton cewa, wannan gasar wasannin ta kasa ba wai kawai za ta bayyana sabbin nasarorin da kasar Sin ta samu a sabon zamani ba ne, har ma za ta nuna dimbin abubuwan ci gaba na zamanantarwa mai salo irin na kasar Sin a yankin Guangdong-Hong Kong-Macao.

A nasu bangaren, Kirsty Coventry da Thomas Bach sun bayyana cewa, kwamitin wasannin Olympics na duniya yana godiya ga kasar Sin saboda goyon bayan da take bayarwa na tsawon lokaci, kuma suna fatan ci gaba da karfafa hadin gwiwa da kasar Sin, tare da inganta ci gaban harkokin wasannin Olympics, da kara yada ruhin wasannin na Olympics a duk fadin duniya, da karfafa hadin kai tsakanin al’ummomin dukkan kasashe, da kuma inganta zaman lafiya a duniya.

Kazalika, duk dai a wannan rana, Xi ya gana da wakilan rukunonin gwajin al’amura da na daidaikun mutane a fannin wasanni na kasa da na gasar wasannin motsa jiki, kafin bude gasar wasannin ta kasa ta karo na 15 a Guangzhou. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032 November 9, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji November 9, 2025 Daga Birnin Sin Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15 November 9, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: wasannin Olympics gasar wasannin a kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa  November 8, 2025 Daga Birnin Sin Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi November 8, 2025 Daga Birnin Sin Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne November 8, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025
  • CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032
  • Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15
  • Mataimakin Shugaban Majalisar Kebbi ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki
  • Dan Wasan Taekwando Na Kasar Iran Abulfazl Zandi Ya Zamo Shi Ne Na Daya A Duniya
  • Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko
  • Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi a Aso Rock
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump