Aminiya:
2025-11-06@08:04:27 GMT

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir

Published: 6th, November 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Cutar basir na daga cikin cututtukan da mutane da dama ke da mabanbantan ra’ayoyi akan ta.

 

A lokuta da dama za ka ji yadda mutane ke fadin dalilai daban daban da ke janyo cutar basir, yayin da wasu ke ganin yawan zama ne ke kawo ta, wasu kuwa gani suke yi zaki da maiko ne ke kawo ta.

Wannan shine abun da da yawa daga cikin mutane suka sani kan wannan cuta, sai dai masana kiwon lafiya na da nasu fahimtar daban kan wannan cuta.

NAJERIYA A YAU: Rashin aikin yi da hanyoyin magance su a Najeriya DAGA LARABA: Yadda ‘Yanbindiga Ke Amfani Da Hakar Zinare Wajen Mallakar Makamai

Shirin Najeriya  A Yau na wannan lokaci zai tattauna ne kan cutar basir da hanyoyin magance ta.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Cutar basir

এছাড়াও পড়ুন:

Barazanar Trump: Ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Nijeriya — Tuggar

Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya gargaɗi Shugaban Amurka Donald Trump, kan kada ya ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Najeriya bayan zargin da ya yi na cewa ana yi wa Kiristoci kisan kiyashi a ƙasar.

Mista Tuggar, wanda ya yi jawabi a taron manema labarai a birnin Berlin tare da takwaransa na ƙasar Jamus, Johann wadephul, yana mai cewa Najeriya ƙasa ce mai bin doka da tsarin mulki, wadda ke tabbatar da cikakken ’yancin addini ga dukkan ’yan ƙasa.

Dalilin da Trump ya yi iƙirarin ana kisan Kiristoci a Nijeriya — Ndume Ousmane Dembele zai buga wasan PSG da Bayern Munich

“Kundin tsarin mulkin Najeriya da dokokin ƙasa sun haramta cin zarafin addini, kuma suna tabbatar da damar kowane ɗan ƙasa ya gudanar da addininsa cikin walwala da kwanciyar hankali,” in ji shi.

Ya ce babu yadda za a yi gwamnatin Najeriya ta goyi bayan duk wata hanya da za ta janyo cin zarafin mabiya wani addini, ko rikicin da zai haifar da tashin hankali irin wanda ya ruguza Sudan.

“Abin da muke so duniya ta fahimta shi ne, ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Najeriya. Ƙasarmu tana da yawan al’umma sama da miliyan 230, kuma ita ce ƙasa mafi girma ta dimokraɗiyya a Afirka,” a cewarsa.

Ya ƙara da cewa lokaci ya yi da ƙasashen waje za su bar ’yan Afirka su warware matsalolinsu da kansu, musamman Najeriya wadda ke cikin kwamitin tsaro na Kungiyar Tarayyar Afirka.

Rahotanni sun tabbatar da cewa, yaƙin da ake fafatawa a ƙasar Sudan da ya yi sanadin mutuwar dubun-dubatar mutane tare da raba wasu miliyoyi da matsugunansu cikin shekaru biyu da suka gabata, inda yanzu haka yaƙin ya bazu zuwa wasu yankunan ƙasar, lamarin da ya haifar da fargabar barkewar wani mummunan bala’i na jin kai.

Barazanar Trump

A ranar Juma’ar da ta gabata ce Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Kiristocin Nijeriya suna fuskantar “barazanar gushewa” sakamakon kisan gillar da ake yi musu lamarin da ya ce shi ya sanya shi saka ƙasar a cikin ƙasashen da “ake matuƙar nuna damuwa a kansu.”

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 ba tare da ya bayyana takamaimai inda ya samu waɗannan alƙaluma ba.

Trump ya ɗauki matakin ne duk kuwa da cewa kwanakin baya mai ba shi shawara kan harkokin Afirka, Mossad Bullos, ya yi watsi da iƙirarin da ke cewa ana yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa
  • Likitoci sun wayar da kan mata kan cutar Sankara a Gombe
  • Matan 500 Za Su Amfana da Gwajin Cutuka Kyauta a Jihar Gombe
  • Barazanar Trump: Ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Nijeriya — Tuggar
  • Dalilin da Trump ya yi iƙirarin ana kisan Kiristoci a Nijeriya — Ndume
  • China ta yi martani kan barazanar Trump ta kai hari Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Barazanar kawo hari abin ɗaga hankali ne ga duk ’yan Nijeriya — Peter Obi
  • NAJERIYA A YAU: Ko Kawo Dakarun Kasar Amurka Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?