Samun rinjayen da APC ta yi na kaso biyu bisa uku a dakunan majalisa biyu yana da babban tasiri ga tsara dokoki, gyaran kundin tsarin mulki da kuma tsarin iko a cikin majalisar tarayya.

Dangane da gyare-gyaren kundin tsarin mulki, bisa sashe na 9 (2) da (3) na kundin tsarin mulki na 1999 (kamar yadda aka gyara), kowane kudiri da ke neman canza kundin tsarin mulki dole ne ya sami goyon bayan akalla kashi biyu cikin uku na dukkan mambobin kowanne majalisa kuma a tabbatar da kashi biyu cikin uku na majalisun jihohi 36 (jihohi 24).

Bisa adadin mambobinta a yanzu, cikin sauki APC na iya tura dokokin gyaran kundin tsarin mulki a majalisar tarayya, ko da yake amincewar matakin jiha na ci gaba da kasancewa wani shinge da ake bukata.

Haka kuma, dangane da tsige shugaban kasa ko mataimakinsa, sashe na 143 (4) da (9) na kundin tsarin mulki na bukatar rinjaye na kaso biyu bisa uku a dukkan majalisu biyu don cire shugaban kasa ko mataimakin shugaban kasa saboda aikata laifuka masu tsanani. A hali ynzu dai, jam’iyyar APC tana iya kare shugaban kasa daga kowace yunkurin tsige shi, domin ‘yan majalisa na adawa ba su da yawan da za su iya yunkurin tsige shugaban kasa ko mataimakinsa.

Kazalika, dangane da cire duk wani babbab jami’an gwamntin kuwa, sashe na 50 (2)(c) da 92 (2)(c) na kundin tsarin mulki sun tanadi cewa shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai ko mataimakansu za a iya cire su ne kawai da rinjaye na kashi biyu cikin uku na majalisunsu. Wannan yana nufin cewa a halin yanzu manyan jami’an gwamnati na iya samun goyon bayan rinjayen APC mai yawa wajen samun kariya daga kokarin korarsu daga mukamansu.

Idan za a ayyanawa ko tsawaita dokar ta-baci a jiha, sashe na 305 (6) na kundin tsarin mulki yana bukatar rinjaye na kashi biyu bisa uku na kowanne majalisar domin shugaban kasa ya sanar ko tsawaita dokar ta-baci a jiha. Bisa samun gagarumin rinjaye, APC ka iya jagorantar majalisa na amincewa da irin wannan bukata cikin sauki, wanda ke ba shugaban kasa karin iko wajen harkokin tsaro na kasa ko rikice-rikicen siyasa.

Idan za a iya tunawa a lokacin muhawarorin da suka shafi ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas, majalisar dattawa ta fara dakatarwa saboda rashin samun yawan kuri’u kashi biyu bisa uku, yayin da majalisar wakilai ta amince da shi ne bayan cike ka’idojin aiki.

A yanzu APC na da ikon yanke hukunci a dukkan majalisun biyu, jam’iyyar mai mulki tana da damar zartar da muhimman hukunci bisa karancin bangaren ‘yan adawa.

A yayin da yake yin sharhi kan samun rinjayar jam’iyyar APC mai mulki da kuma ikonta a majalisar tarayya kafin zaben 2027, wani masanin siyasa, Farfesa Gbade Ojo, ya yi gargadi kan kalubalen da makomar dimokuradiyyar Nijeriya zai iya fuskanta.

“Abin da muke shaidawa shi ne, ci gaba da fadada jam’iyyar APC mai mulki. Duk da cewa hakan na iya bayyana a matsayin karfin siyasa a fili, tasirinsa ga dimokuradiyya abin damuwa ne sosai,” in ji shi.

Ya yi gargadin cewa a irin wannan yanayi, majalisar kasa na iya rasa ‘yancinta tare da zama ‘yar amshin shadar bangaren zartarwa. Ya ce idan har ‘yan adawa ba su tashi tsaye ba, to dimokuradiyyar Nijeriya za ta ci gaba da zama cikin hadari.

2027: Rikicin PDP Ya Kara Kazanta Yayin Da Aka Sake Samun Rarrabuwar Kai A Jam’iyyar

Jam’iyyar PDP ta sake fuskantar kazamin rikici bayan da babbar kotun tarayya a Abuja ta dakatar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), daga amincewa da shirya babban taron jam’iyyar da aka shirya a Ibadan, Jihar Oyo.

Alkali James Omotosho ya bayar da umarnin hana wasu ayyuka yayin da yake yanke hukunci kan wani kara da ya kalubalanci halaccin taron da aka shirya, hukuncin dai ya sake sama tsofaffin raunuka jam’iyyar tare da janyo kazamin rarrabuwan kawuna a cikin babban jam’iyyar adawar ta Nijeriya.

Duk da hukuncin, shugabannin PDP sun dage cewa taron zai gudana kamar yadda aka tsara, suna bayyana hukuncin a matsayin cin fuska ga dimokuradiyya ta cikin gida da kuma tauye hakkin kundin tsarin mulkinsu na gudanar da harkokinsu na jam’iyya.

A cikin martanin kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar, ya sanar da dakatar da manyan jami’ai, ciki har da sakataren jam’iyyar na kasa, Samuel Anyanwu da sakataren shirye-shiryenta na kasa, Umar Bature da mashawarcin shari’a na kasa, Kamaldeen Ajibade da mataimakin mashawarcin shari’a na kasa, Okechukwu Osuoha saboda zargin karya kundin tsarin jam’iyyar.

Amma lamarin ya dauki sabon salo lokacin da wani bangare na jam’iyyar ya fitar da nasa jerin sunayen wadanda ya dakatar, wannan karon yana nufin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum da sakatar yada labarai, Debo Ologunagba da wasu mutum hudu duk an dakatar da su, wanda lamarin ya kara rikitarwa game da wanda yake da cikakken iko a cikin PDP.

Wasu majiyoyi daga cikin PDP sun nuna cewa hana tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido, takarar shugabancin jam’iyyar na daya daga cikin musabbabin sabon rikicin.

“Lamido yana daya daga cikin wadanda suka ki shiga ayyukan PDP a baya har sai an dakatar da Wike. Yanzu an gan shi yana hada kai da masu goyon bayan Wike, wanda ke nuna inda sababbin rikicin ya sake kunno kai,” in ji wata majiya.

A cewar wata majiya ta daban, yunkurin Lamido na sayen fam din takarar shugaban jam’iyyar a makare wata alama ce na cewa akwai lauje cikin nadi.

“Ana sayar da fam a Gidan Legacy, ba a Wadata Plaza ba. An fara sayar da fam din ne tun a ranar 2 ga Satumba kuma an rufe a ranar 22 ga Satumba, tare da kara lokacin mika fam din har zuwa 27 ga Oktoba. To ta yaya mutum zai iya zuwa a ranar karshe ya yi ikirarin cewa bai samu fam ba?” in ji majiyar.

Yayin da PDP ke fama da shari’o’I a kotu, dakatar da juna da kuma tawaye na rarrabuwar kai, masu ruwa da tsaki a jam’iyya suna cewa babban kalubale yanzu shi ne sake gina sahihancin jam’iyyar da hadin kai kafin 2027.

Manyan jiga-jigan jam’iyya sun yi gargadin cewa idan ba a samu sulhu da jagoranci mai kyau ba, jam’iyyar adawa na iya fuskantar karin rarrabuwan kawuna kafin zaben 2027.

Ga jam’iyyar adawa mafi shahara a Nijeriya ta PDP, a halin yanzu aikin ya wuce kawai shirya babban taro, yana da alaka da dawo da aminci da hadin kai da kuma karfafa alaka kafin zaben 2027.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tambarin Dimokuradiyya Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta October 17, 2025 Tambarin Dimokuradiyya 2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara October 17, 2025 Tambarin Dimokuradiyya Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe October 10, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: na kundin tsarin mulki majalisar tarayya a majalisar jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya ce Gwamnatin Tarayya ta buɗe kofofin tattaunawa da ƙasashen duniya, ciki har da Amurka, dangane da barazanar kasar ta kaddamar da yaki a Najeriya.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa bayan taron Majalisar Zartarwa ta Ƙasa da Shugaba Bola Tinubu ya jagoranta, Ministan ya ce gwamnatinsu ba ta son ƙara yin yamadidi da maganar.

An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8 Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa

“Babban nauyin da ke kanmu a matsayin gwamnati shi ne tabbatar da cewa gwamnatin Najeriya za ta ci gaba da ɗaukar mataki a kan duk wata damuwa ta gaskiya da ke da alaƙa da tsaron ’yan ƙasa.

“Amma ba ma cikin yanayin firgici. Muna mayar da martani cikin natsuwa, hankali, da kuma la’akari da muradun ƙasarmu, tare da duba damuwar da ke cikin gida da waje dangane da halin da ake ciki. Amma zan sake jaddadawa, Najeriya ƙasa ce mai ba da ’yancin yin addinai,” in ji ministan.

Ya kuma ce gwamnati na mayar da martani kan waɗannan batutuwa ta hanyar kiyaye mutunci da darajar ƙasar, da kuma haɗin gwiwa da kowa, ciki har da ƙasashen duniya, don magance wannan matsala.

“Muna da iyakoki masu sauƙin shigowa, shi ya sa muke da fahimtar juna da makotanmu. Haka kuma muna da haɗin gwiwa da ƙasashen duniya, ciki har da Amurka, kuma Najeriya za ta ci gaba da tattaunawa. Mun fara magana da gwamnatin Amurka. Hanyoyin sadarwar mu a bude suke. Muna so a warware wannan matsala ta hanyar diflomasiyya.

“Baya ga siyasar lamarin, muna ɗaukar batun da muhimmanci. Amma ina so in ƙara jaddada cewa gwamnati, tun kafin abubuwan da suka faru a kwanakin baya, ta jajirce matuƙa wajen tabbatar da cewa Najeriya ƙasa ce amintacciya ga kowa.

“Shin akwai matsalolin tsaro a ƙasa? Eh, akwai. Shin ana kashe mutane a wasu sassan ƙasa? Eh. Amma shin gwamnati na yin wani abu don dakile hakan? Eh, tabbas akwai. Shin gwamnati na mayar da martani? Eh, tana yi. Amma ana yin hakan cikin cikakken hanyoyin da suka dace, tare da kiyaye daidaito da ake buƙata don fuskantar waɗannan matsaloli kai tsaye,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Yaduwar Juyin Mulki A Afirka
  • Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu