Saudiyya ta zaftare wa Najeriya guraban Aikin Hajji da sama da kujeru 28,000
Published: 17th, October 2025 GMT
Kasar Saudiyya ta rage yawan guraben kujerun aikin hajjin da take ware wa Najeriya daga 95,000 zuwa 66,910 daga shekarar 2026.
Aminiya ta ruwaito cewa a baya Najeriya ta shafe tsawon shekaru uku tana samun guraben na 95,000 a yayin Aikin Hajjin.
’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 8 a harin kwanton ɓauna a Zamfara An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a BauchiA cewar Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), wannan sauyi ya biyo bayan gazawar Najeriya wajen cika guraben da aka ware mata a hajjin shekarun 2024 da 2025.
Wata sanarwa da, Mataimakiyar Darakta a Sashen Yaɗa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara, ta sanya wa hannu, ta ce hakan na nufin za a sake fasalin yadda za a raba guraben zuwa jihohi, bisa la’akari da yawan alhazan da kowace jiha ta kai a hajjin 2025.
“Shafin Aikin Hajji na Saudiyya ya nuna cewa guraben da aka ware wa Najeriya a hajjin 2026 sun kai 66,910. Wannan na nufin cewa duk da an ware gurabe 95,000 ga Najeriya, adadin da za su iya tafiya hajji a 2026 bai wuce 66,910 ba. An ce an rage guraben ne saboda rashin cikakken amfani da su a shekarar da ta gabata,” in ji sanarwar.
Bayanin na zuwa ne bayan wani taro tsakanin NAHCON da wakilan jihohi domin tattaunawa kan farashin kujerar Aikin Hajji da wasu muhimman batutuwa.
Kwamishinan Ayyuka na NAHCON, Prince Anofiu Elegushi, ya ce za a sake duba rabon guraben da aka yi a baya bisa la’akari da yadda kowace jiha ta yi amfani da gurabenta a hajjin 2025.
A jawabinsa na buɗe taron, Shugaban Hukumar NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya yi kira da a haɗa kai domin tabbatar da nasarar shirya hajjin 2026.
Ya kuma jaddada buƙatar shugabannin hukumomin jin dadin alhazai na jihohi su ɗauki batun binciken lafiyar alhazai da muhimmanci, duba da yadda Saudiyya ita ma ke ɗaukar lamarin da matuƙar muhimmanci.
A yayin taron, NAHCON ta ce tana ci gaba da tattaunawa da hukumomi domin rage wasu kuɗaɗe kamar na jigilar kaya, don rage yawan kuɗin da ke kan masu niyyar zuwa hajji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya sake aike wa Majalisar Dattawa ƙarin sunayen mutum 32 domin tantance su a matsayin jakadu.
Sunayen sun haɗa da manyan mutane kamar tsohon shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Femi Fani-Kayode, da Reno Omokri.
Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a GombeAn raba sunayen zuwa kashi biyu; na farko yana ɗauke da sunan mutum 15 waɗanda suke da gogewar aikin jakadanci da kuma waɗanda ba su gogewar aikin jakadanci mutim 17.
Wasu daga cikin fitattu da suka shiga jerin sun haɗa da tsofaffin gwamnonin kamar Ifeanyi Ugwuanyi da Victor Okezie Ikpeazu, matan tsofaffin gwamnoni kamar Angela Adebayo da Florence Ajimobi, da kuma Sanata Jimoh Ibrahim.
Bayan tantancewa, za a tura jakadun zuwa ƙasashe irin su China, Indiya, Kanada, UAE, Afrika ta Kudu, da Kenya.
Sauran wuraren sun haɗa da manyan cibiyoyi na ƙasa da ƙasa kamar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), UNESCO, da Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU).
Za a bayyana inda za a tura kowane, bayan Majalisar Dattawa ta tantance su.
A makon da ya gabata ne, Tinubu ya tura sunayen mutum uku da ake sa ran tura su Amurka, Birtaniya ko Faransa.
Shugaban ya ce za a sake fitar da ƙarin sunayen jakadu nan ba da jimawa ba.
Wannan mataki na cikin shirin Tinubu na karfafa hulɗar diflomasiyya ta hannun ƙwararru da gogaggun mutane don wakiltar Najeriya a ƙasashen waje.
Ana sa ran Majalisar Dattawa za ta fara tantance su cikin makonni masu zuwa, kafin su kama aiki.
Masu sharhi kan sha’anin siyasa suna ganin waɗanda aka zaɓo ƙwararru ne kuma za su taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasar gida da waje.
Da dama na ganin cewa waɗannan naɗe-naɗen za su iya taka rawa wajen tsara sabuwar hanyar hulɗa da ƙasashen waje da manufofin diflomasiyyar Najeriya a nan gaba.