Bishop Matthew Kukah, na Cocin Katolika da ke Jihar Sakkwato, ya ce barazanar da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na kawo wa Najeriya ya farkar da shugabannin ƙasar nan. 

Trump, ya zargi Najeriya da cin zarafin Kiristoci tare da barazanar janye tallafin Amurka ko kuma ɗaukar matakin soja domin “ceto Kiristoci” a ƙasar.

Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi a Aso Rock Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu — Tinubu

Sai dai Shugaba Bola Tinubu, ya musanta wannan zargi, inda ya bayyana cewa Najeriya kasa ce mai cikakkiyar dimokuraɗiyya mai mutunta ’yancin yin addini.

Da yake jawabi a wajen bikin cika shekaru 60 na ɗan jarida Reuben Abati a Jihar Legas, Kukah, ya ce kalaman Trump na nuna akwai matsaloli a Najeriya.

“Muna ganin Trump a matsayin  matsala. Amma Trump alama ce ta rashin lafiyar da ke cikin ƙasarmu,” in ji Kukah.

“Ko Trump ne ko wani daban ya tunzuramu, lokaci ya yi da Najeriya za ta farka.”

Ya kuma soki rashin wuraren yawon buɗe ido da abubuwan tarihi da za su nuna ainihin abubuwan da Najeriya ta mallaka.

“Idan wani ya zo Najeriya yau, ina za ka kai shi? Dole mu sake gina ƙasarmu da kuma bayyana tarinhinmu a matsayin ’yan ƙasa,” in ji shi.

Kukah ya yi kira ga ’yan Najeriya da su yi tunani mai zurfi tare da ɗaukar nauyin gina ƙasa mai haɗin kai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta samu ci gaba sosai wajen magance matsalar rashin tsaro a faɗin ƙasar cikin shekaru biyu da suka gabata.

Shugaban ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na daƙile ayyukan ta’addanci da kuma tabbatar da zaman lafiyar ƙasa.

Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai

A wata sanarwa da Tinubu ya fitar a shafinsa na sada zumunta, a ranar Juma’a, ya ce ƙalubalen tsaro a Najeriya, da suka haɗa da ta’addanci da aikata laifuka, ana magance su da sabbin tsari da sauye-sauyen dabarun dawo da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

“Haƙiƙa muna fuskantar ta’addanci – ƙalubalen da Najeriya ta fuskanta kusan shekaru ashirin, kuma ba za mu ja da baya ba, za mu yi nasara a kan ta’addanci kuma mu yi iƙirarin samun nasara a wannan yaƙin, ba za mu taɓa yin sulhu harkar tsaro ba.

“Najeriya ƙasa ɗaya ce mai haɗin kai, mun tashi tare, mun ci gaba tare, kuma mun ƙi yanke ƙauna domin tabbatar da ƙuduri.

“Aikin da ke gabanmu yana da yawa, amma duk da haka ƙudurinmu ya fi girma, za mu ci gaba da ɗorewa tare da inganta nasarorin da muka samu na sake fasalin ƙasa da kuma samar da ci gaba a Najeriya.

“Ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba kuma ba za mu bar wani abu ba a cikin aikinmu na kawar da masu aikata laifuka a cikin al’ummarmu, muna kira ga abokan haɗin gwiwarmu da su tsaya tsayin daka tare da mu yayin da muke ƙara faɗaɗa yaƙin da muke yi da ta’addanci, mun samu gagarumin ci gaba a cikin shekaru biyu da suka gabata, kuma za mu kawar da wannan barazana.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan
  • Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140