Ya ƙara da cewax gwamnatinsa ta fara gyara daga tushe, inda ilimi ya zama ginshiƙin farko. “Shekaru takwas kafin mu hau mulki, ɗalibanmu ba su samun takardun WAEC, sannan tsawon shekaru biyu suna fama da matsalar NECO. Na biya Naira Biliyan huɗu don magance wannan matsala,” inji shi.

 

Gwamnan ya bayyana irin matsalolin da ya gada, yana mai cewa: “Na samu asusun gwamnati da naira miliyan huɗu kacal.

Ma’aikata suna karɓar albashi cikin rashin tabbas, babu ruwa, asibitoci kuwa suna cikin mummunan yanayi.”

 

Lawal ya ce, ya sake fasalin tsarin gwamnati, inda ya rage yawan kwamishinoni da manyan sakatarorin don rage ɓarna da ƙara inganci. “Yanzu muna daga cikin jihohi mafi ci gaba wajen tara haraji, inda kuɗaɗen shiga suka ƙaru da fiye da kaso 300 cikin 100,” inji shi.

 

Ya bayyana cewa gwamnatin sa ta gina ko ta gyara makarantu sama da 500, tare da aiwatar da ayyukan da kuɗinsu ya kai biliyan N10 a kowace ƙaramar hukuma. Duk da cewa ana cire biliyan 1.2 a kowane wata daga kuɗaɗen gwamnati don biyan basussuka, an biya bashin fansho da giratuti na fiye da biliyan N13.6 da aka tara tun shekarar 2011.

 

A ɓangaren tsaro, Lawal ya ce jihar ta ɗan sami sauƙi bayan kafa rundunar tsaron gida, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin tabbatar da amfanin mulki ya kai ga talaka.

 

A nasa jawabin, Babban Editan LEADERSHIP, Azu Ishiekwene, ya ce an bai wa gwamnan wannan lambar yabo ne saboda irin nasarorin da ya samu a fannonin tsaro, ilimi, lafiya da gine-gine, yana mai cewa “jarida tana da alhakin duba gwamnati, amma kuma tana da haƙƙin yabawa idan ana yin daidai.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sanata Barau Zai Yi Ƙarar Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10 November 8, 2025 Labarai Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta November 8, 2025 Manyan Labarai Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja November 8, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na shiyyar Abuja (AEDC) ya fara aikin rage ma’aikata kusan 800, a daidai lokacin da ’yan Najeriya ke ci gaba da fama da hauhawar farashi, tsadar rayuwa, da rashin tabbas wajen samun wutar lantarki.

Matakin korar wanda ta fara a ranar Laraba, ya biyo bayan watanni na sake fasalin cikin gida a kamfanin da ke ba da wutar lantarki ga Babban Birnin Tarayya Abuja da jihohin Kogi, Neja da Nasarawa.

Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah

Majiyoyi da dama da ke da masaniya kan lamarin sun shaida cewa shugabannin kamfanin sun fara ne da shirin korar ma’aikata 1,800, kafin su rage adadin zuwa 800 bayan jerin tattaunawa masu zafi da Ƙungiyar Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Ƙasa da Ƙungiyar Ma’aikatan Wutar Lantarki da Ƙungiyoyin Kwadago.

Wata majiya daga cikin ma’aikatan AEDC ta ce shugabannin kamfanin sun fara da shirin korar 1,800, amma sun rage zuwa 800 bayan matsin lamba daga ƙungiyoyin, waɗanda a farko suka dage cewa ba a kamata a kori kowa ba.

“Shugabanni sun so su kori 1,800, amma bayan matsin lamba, sun rage zuwa 800. Tun da farko kungiyoyin sun nemi kada a kori kowa,” in ji ma’aikacin da ya nemi a boye sunansa don kauce wa hukunta shi.

“Ƙungiyoyin sun fara da cewa kada a kori kowa, amma daga baya an ce sun amince da 800. Ma’aikatan da abin ya shafa sun kamata su fara karɓar takardunsu daga ranar Litinin, amma an jinkirta, sai jiya aka fara ba su takarda,” wata majiya ta bayyana.

Wata takardar sallama mai taken “Sanarwar Sallama Daga Aiki”, da aka rubuta a ranar 5 ga Nuwamba, 2025, kuma Adeniyi Adejola, Babban Jami’in Kula da Ma’aikata na kamfanin, ya sanya wa hannu, ta tabbatar da cewa aikin na daga cikin “shirin daidaita ma’aikata da ake ci gaba da aiwatarwa.”

Takardar ta kuma bayyana cewa duk ma’aikatan da abin ya shafa za su karɓi haƙƙinsu bayan kammala tsarin sallamar su.

Wani ɓangare na takardar ya ce: “Muna bakin cikin sanar da kai cewa ba za a sake buƙatar ayyukanka a kamfanin nan ba daga ranar 5 ga watan Nuwamba, 2025. Wannan shawara ta biyo bayan sakamakon aikin daidaita ma’aikata da kamfanin ke aiwatarwa. Ka tabbata cewa an yanke wannan shawara bayan dogon nazari da kuma bisa ka’idojin kamfanin.”

“Ana buƙatar ka kammala tsarin sallama a wurin aikinka, ka kuma dawo da duk wani kayan kamfani da ke hannunka kafin ka mika kanka ga wakilin kula da ma’aikata. Kammala waɗannan matakai ne zai ba da damar sarrafa kuɗin sallamarka,” in ji takardar sallamar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
  • Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar
  • Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
  • Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai