Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
Published: 6th, November 2025 GMT
Ko shakka babu, yunkurin kasar Sin na cimma nasarar kawar da fitar da hayakin carbon daga kololuwar matsayinsa nan zuwa shekarar 2060 ya cancanci yabo. Kuma abu ne mai yiwuwa, duba da nasarorin baya da kasar ta cimma, ciki har da nasarar da ta samu ta rage fitar da hayakin na carbon a shekarar 2020 da kaso 60 bisa dari kan na shekarar 2005, adadin da ya haura hasashen nasarar da aka yi fata da karin kaso 40 zuwa 45 bisa dari.
A fannin cimma burikan kafa karin cibiyoyin samar da lantarki ta iska da hasken rana kuwa, yanzu haka kasar Sin ta kai inda take buri, tun ma kafin shekarar 2030 da a baya aka tsara cimma burin hakan. A daya bangaren kuma, tana tallafawa wasu kasashe masu tasowa, karkashin manufofi irin su hadin gwiwar gina shawarar “ziri daya da hanya daya”, wajen aiwatar da dabarun dakile sauyin yanayi, da jure tasirinsa, da aiwatar da dubban matakai masu nasaba da hakan.
Tabbas kowa ya yarda cewa shawo kan kalubalen sauyin yanayi na bukatar hadin gwiwar dukkanin sassa, kuma la’akari da gudunmawar da Sin ke bayarwa a gida da waje, ma iya cewa tana kan turbar jagorantar duniya wajen cimma nasarar hakan ta yadda za a gudu tare a tsira tare, wato a kai ga cin gajiyar kyakkyawan muhallin duniya mai kayatarwa. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta yi tsokaci game da matakin Amurka na sanya Najeriya cikin jerin kasashen da ake da damuwa a kansu, inda ta jaddada matsayin Sin na matukar goyon bayan gwamnatin Najeriya, wajen jagorantar al’ummarta zuwa turbar neman ci gaba bisa yanayin da kasar ke ciki.
A ’yan kwanakin nan ne shugaban Amurka Donald Trump, ya sanar da sanya Najeriya cikin jerin kasashen da kasarsa ke kara mayar da hankali a kansu, bisa zargin barazanar da ya ce mabiya addinin Kirista na fuskanta a kasar. Trump ya kara da cewa, idan har gwamnatin Najeriyar ta gaza shawo kan kisan Kiristoci, to Amurka za ta hanzarta dakatar da dukkanin tallafin da take baiwa kasar, kana za ta kaddamar da matakan soji a Najeriyar.
To sai dai kuma a nata martani, ma’aikatar harkokin wajen Najeriyar ta fitar da wata sanarwa, wadda ke musanta zargin na Amurka, tare da jaddada cewa Najeriya na ci gaba da yaki da ayyukan masu tsattsauran ra’ayi, da kare rayukan ’yan kasar, da martaba rayukan mabiya mabambantan addinai da akidu, kana tana biyayya ga dokoki daidai da odar kasa da kasa.
Cikin amsar da ta bayar dangane da tambayar wani dan jarida, Mao Ning ta ce kasar Sin na adawa da wata kasa ta tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wasu kasashe na daban, ta hanyar fakewa da batun kare hakkokin addini ko na bil’adama. Kazalika, tana adawa da yawaitar barazanar kakaba takunkumai da amfani da karfin tuwo. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA