Aminiya:
2025-11-02@17:02:12 GMT

Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci

Published: 2nd, April 2025 GMT

Wani basakkwace, Musa Abubakar, wanda a bayan nan ya yi ridda saboda zullumin ’yan bindiga masu kai hare-hare da ta’adar garkuwa da mutane, ya sake karɓar addinin Musulunci.

A ranar Asabar ce mutumin tare da matansa biyu suka sake karɓar addinin Islama bayan  ridda da suka yi a kwanan baya.

Tinubu zai tafi ziyarar makonni biyu a Faransa Kisan Mafarauta: Babu wanda aka kai wa harin ramuwar gayya a Kano — Ƙungiyoyin Matasa

Bayanai sun ce Musa Abubakar ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Sabon Birni da ke Sakkwato ya yi ƙaura zuwa Jihar Taraba a sakamakon yanayin tsaro a mazauninsa.

Bayan komawa Taraba ne kuma ya shawarci matansa uku da su  karɓi addini Kiristanci, kuma ya yi nasara biyu suka amince.

Sai dai wannan lamari ya tayar da ƙura musamman a Sakkwato, inda har ta kai ga Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko ya haɗa kwamitin malamai domin su faɗakar da Musa kan ridda da ya yi.

Aminiya ta ruwaito cewa mambobin kwamitin sun haɗa da Alƙalin Alƙalai na Sakkwato, Malam Ahmad Umar Helele da Sarkin Malamai, Malam Yahya Na-Malam da kuma Malam Bashir Gidan Kanawa a matsayin sakataren kwamitin.

A yayin ganawa da mambobin kwamitin, Musa Abubakar ya shaida musu dalilan da suka fusata shi ya yi ridda ya koma Kirista.

Da yake zantawa da manema labarai kan binciken kwamitin, Malam Gidan Kanawa ya bayyana cewa, Musa Abubakar yana da ƙarancin ilimin addini baya ga rasa sana’arsa da ta’addancin ’yan bindiga ya haddasa.

“Wannan lamari ne ya fusata shi, ya jefa shi cikin ƙuncin rayuwa kuma ya yanke shawarar ƙaura zuwa Taraba, inda a nan aka yi amfani da tallafin kuɗi wajen kwaɗaita masa shiga Kiristanci,” in ji shi.

Da yake bayyana halin da shiga, Musa Abubakar ya ce ya yi ridda ne watanni kaɗan da suka gabata, amma a yanzu ya sake karɓar addinin Islama a sakamakon faɗin tashin da ’yan uwansa da malamai da shugabanni suka yi.

“A yanzu na dawo na karɓi addina na Islama tare da iyalina. Na yi nadamar abin da na aikata da kuma damuwar da na jefa ’yan uwa da malamai.

“Yamzu ga ni na dawo Sakkwato kuma zan ci gaba da sana’a da sauran harkokin kasuwanci,” in ji Musa. Ya sha alwashin cewa shi da iyalansa za su sadaukar da rayuwarsu a kan addinin Islama. A nasa jawabin, wani yayan Musa Abubakar, Alhaji Adamu Sabon Birni, ya ce “ta’addancin ’yan bindiga masu garkuwa da mutane ne ya yi ajalin mahaifina.

“’Yan bindiga ne suka kashe shi bayan karɓa kuɗin fansa har Naira miliyan 9 amma hakan bai sa na yi ridda ba, saboda matsalar ta’addancin ’yan bindiga ba iya Sakkwato kaɗai ake fama da ita ba.

“A duk faɗin Arewa ana fuskantar wannan matsala kuma mahukunta na iya ƙoƙarinsu wajen magance ta.

“Saboda haka a yanzu muna farin ciki ya gane kuskuren da ya yi kuma ya sake karɓar addinin Musulunci.

Matan Musa Abubakar da aka zanta da su sun ce za su iya ƙoƙari wajen goyon bayan mijinsu don ganin ya ci gaba da zama a Sakkwato kuma ya dawwama a kan tafarkin addinin Islama.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato Jihar Taraba Musa Abubakar ya sake karɓar addinin Musa Abubakar ya yi ridda yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

“Haka kuma an kama wata mata mai shekaru 34 da ake zargi da hannu a lamarin, tare da wasu masu gidan marayu guda biyu da ke Abuja da Jihar Nasarawa, inda aka gano wasu yaran da ake kyautata zaton an yi safarar su. Wasu daga cikin gidajen marayun da aka gano ana amfani da su ne a matsayin cibiyoyin ajiye yara, inda ake jiran ‘kwace’ ko sayar da su da sunan daukar nauyin marayu.”

Ya ce, “An gano gidajen marayu guda hudu da ke Kaigini, Kubwa Edpressway Abuja; Masaka Area 1, Mararaba kusa da Abaca Road; da kuma Mararaba bayan Kasuwar Duniya suna da alaka da wannan kungiya, kuma ana ci gaba da bincike a kansu.”

Ya kara da cewa, daya daga cikin masu korafin ya bayyana cewa ya biya Naira miliyan 2.8 a matsayin kudin daukar yaro, sannan ya biya Naira 100,000 a matsayin kudin shawara ga daya daga cikin ‘yan kungiyar.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wani mai korafi ya ce shi ma ya biya Naira miliyan 2.8 kudin daukar yaro da Naira 100,000 kudin shawara ga wani dan kungiyar.

“An canza sunayen yawancin yaran da aka ceto, lamarin da ya kara wahalar da bincike da gano asalinsu,” in ji sanarwar.

Darakta Janar ta NAPTIP, Binta Adamu Bello, ta bayyana damuwarta kan wannan lamari, inda ta ce safarar yara ta zama babbar matsala a kasa.

Ta hanyar Adekoye, DG din ta nuna damuwa game da yadda wasu gidajen marayu ke amfani da raunin jama’a wajen aiwatar da safarar yara.

Ta ce, “Abin takaici ne yadda wasu masu mugunta da ke da sunayen kwararru da matsayi a cikin al’umma, suke amfani da matsayin su wajen yaudarar mutanen da ke cikin mawuyacin hali, su yi safarar ‘ya’yansu, da dama daga cikinsu ma sun tsira ne daga halaka a lokacin rikice-rikicen al’umma ko na manoma da makiyaya, sannan a sayar da su ga iyaye masu neman haihuwa a matsayin daukar yaro ba tare da sahihin izinin iyayensu ba.

“Wannan abin ba za a yarda da shi ba, kuma wadanda aka kama kan wannan mugun aiki za su fuskanci hukuncin doka yadda ya kamata.

“’Ya’yanmu ba kayayyaki ba ne da za a ajiye su a gidajen marayu a sayar ga mai biyan mafi tsada. Wannan dole ya tsaya,” in ji ta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa November 1, 2025 Manyan Labarai Jerin Gwarazan Taurarinmu November 1, 2025 Manyan Labarai Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma