Aminiya:
2025-06-15@08:27:25 GMT

Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci

Published: 2nd, April 2025 GMT

Wani basakkwace, Musa Abubakar, wanda a bayan nan ya yi ridda saboda zullumin ’yan bindiga masu kai hare-hare da ta’adar garkuwa da mutane, ya sake karɓar addinin Musulunci.

A ranar Asabar ce mutumin tare da matansa biyu suka sake karɓar addinin Islama bayan  ridda da suka yi a kwanan baya.

Tinubu zai tafi ziyarar makonni biyu a Faransa Kisan Mafarauta: Babu wanda aka kai wa harin ramuwar gayya a Kano — Ƙungiyoyin Matasa

Bayanai sun ce Musa Abubakar ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Sabon Birni da ke Sakkwato ya yi ƙaura zuwa Jihar Taraba a sakamakon yanayin tsaro a mazauninsa.

Bayan komawa Taraba ne kuma ya shawarci matansa uku da su  karɓi addini Kiristanci, kuma ya yi nasara biyu suka amince.

Sai dai wannan lamari ya tayar da ƙura musamman a Sakkwato, inda har ta kai ga Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko ya haɗa kwamitin malamai domin su faɗakar da Musa kan ridda da ya yi.

Aminiya ta ruwaito cewa mambobin kwamitin sun haɗa da Alƙalin Alƙalai na Sakkwato, Malam Ahmad Umar Helele da Sarkin Malamai, Malam Yahya Na-Malam da kuma Malam Bashir Gidan Kanawa a matsayin sakataren kwamitin.

A yayin ganawa da mambobin kwamitin, Musa Abubakar ya shaida musu dalilan da suka fusata shi ya yi ridda ya koma Kirista.

Da yake zantawa da manema labarai kan binciken kwamitin, Malam Gidan Kanawa ya bayyana cewa, Musa Abubakar yana da ƙarancin ilimin addini baya ga rasa sana’arsa da ta’addancin ’yan bindiga ya haddasa.

“Wannan lamari ne ya fusata shi, ya jefa shi cikin ƙuncin rayuwa kuma ya yanke shawarar ƙaura zuwa Taraba, inda a nan aka yi amfani da tallafin kuɗi wajen kwaɗaita masa shiga Kiristanci,” in ji shi.

Da yake bayyana halin da shiga, Musa Abubakar ya ce ya yi ridda ne watanni kaɗan da suka gabata, amma a yanzu ya sake karɓar addinin Islama a sakamakon faɗin tashin da ’yan uwansa da malamai da shugabanni suka yi.

“A yanzu na dawo na karɓi addina na Islama tare da iyalina. Na yi nadamar abin da na aikata da kuma damuwar da na jefa ’yan uwa da malamai.

“Yamzu ga ni na dawo Sakkwato kuma zan ci gaba da sana’a da sauran harkokin kasuwanci,” in ji Musa. Ya sha alwashin cewa shi da iyalansa za su sadaukar da rayuwarsu a kan addinin Islama. A nasa jawabin, wani yayan Musa Abubakar, Alhaji Adamu Sabon Birni, ya ce “ta’addancin ’yan bindiga masu garkuwa da mutane ne ya yi ajalin mahaifina.

“’Yan bindiga ne suka kashe shi bayan karɓa kuɗin fansa har Naira miliyan 9 amma hakan bai sa na yi ridda ba, saboda matsalar ta’addancin ’yan bindiga ba iya Sakkwato kaɗai ake fama da ita ba.

“A duk faɗin Arewa ana fuskantar wannan matsala kuma mahukunta na iya ƙoƙarinsu wajen magance ta.

“Saboda haka a yanzu muna farin ciki ya gane kuskuren da ya yi kuma ya sake karɓar addinin Musulunci.

Matan Musa Abubakar da aka zanta da su sun ce za su iya ƙoƙari wajen goyon bayan mijinsu don ganin ya ci gaba da zama a Sakkwato kuma ya dawwama a kan tafarkin addinin Islama.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato Jihar Taraba Musa Abubakar ya sake karɓar addinin Musa Abubakar ya yi ridda yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

Semenyo ma ya taka rawar gani saboda kwallo biyun da ya ci a wasan karshe sun sa ya ci wa kungiyarsa Bournemouth kwallo 11 kenan a karonfarko.

Danwasan Najeriya Aled Iwobi ya fi abokan wasansa kokari a Fulham da kwallayensa tara da ya ci da kuma taimakawa wajen cin shida, sannan ya dan dara Amad Diallo na Manchester United (wanda ya ci takwas kuma ya bayar aka ci shida). Amma Iwobi ya fi shi buga wasanni saboda Diallo ya yi jinyar wajan watanni uku a kakar da ta gabata. Iwobi ne dai kan gaba wajen kirkirar damarmaki (59) da kuma bayar da cikakken fasin (508) a cikin bangaren abokan hamayya, inda shi kuma.

Thomas Partey na Ghana ya fi yawan tura cikakkun fasin (1,631). Shi kuwa Idrissa Gana Gueye ya nuna bajintarsa ne wajen taimka wa Eberton samun damar ci gaba da zama a gasar. Dan Senegal din mai shekara 35 ya cim ma mafi girman bajintar dakatar da abokan hamayya sau 133 kuma ya dauke kwallo daga abokin hamayya sau 221, inda ya zarta kowane dan kwallo daga nahiyar Afrka.

Aaron Wan-Bissaka, shi ne ya fi kowa tare kwallo (66) kuma ya fi yawan yin yanka (64) a ‘yanwasan bayan Premier League – hakan ya sa magoya bayan West Ham suka zabe shi gwarzonsu a bana. Dan Ajeriya Rayan Ait-Nouri, wanda ya koma kungiyar Manchester City a wannan watan ya nuna bajintar kai hari duk da matsayinsa na danwasan baya ta gefe, inda ya ci wa tsohuwar kungiyarsa ta Wolbes kwallo hudu kuma ya bayar aka ci bakwai.

Dan wasa Ola Aina ya taka rawa mafi kyau a tarihi sana’arsa a Nothingham Fores, inda ya dinga kwalo daga ƙafar abokan hamayya sau 190 – mafi yawa kenan da wani danwasan baya ya taba yi. Dan Najeriyar mai buga baya a bangaren dama ya cire kwallo daga kan layin shiga raga sau uku, wanda ‘yanwasa shida ne kawai suka iya yin irin wannan bajintar cikinsu kuma har da Iliman Ndiaye na Senegal.

Calbin Bassey na Najeriya ya taba kwallo sau 2,536 a Fulham – fiye da kowane dankwallon Afirka kenan a gasar – da cikakken fasin 1,926 da ya bayar, da tsige kwallo sau 113, da hana kwallo wucewa sau 17. A gefe guda kuma, Noussair Mazraoui ya tare abokan hamayya sau 115 da kuma dauke kwallo sau 216 daga abokin hamayya a Manchester United.

Andre Onana, mai tsaron raga dan Afirka tilo a Premier League, ya fuskanci kalubale mai girma a kakar bana yayin da Manchester United ta shiga tasku mafi muni cikin shekara 50. Mai tsaron ragar na Kamaru ya buga wasa tara ba tare da an zira masa kwallo a raga ba, amma kuma an ci shi kwallo 44 cikin wasa 25. Hana kwallo shiga raga sau 90 da ya yi shi ne karo na 12 kuma mafiya yawa,

inda adadin ya zama kashi 66 cikin 100 kuma na 15 kenan a tsakanin masu tsaron da suka buga wasa 10 ko fiye da haka. Danwasan mai shekara 29 ya yi kuskure uku da suka jawo zira masa kwallo a raga – ‘yanwasa uku ne kawai suka yi fiye da hakan.

 

Tarihi mara amfani

Danwasan da ya fi kowa yin keta a kakar Premier ta 2024-25 shi ne, Semenyo na Bournemouth, wanda aka busa wa laifi sau 73. Adadin ya zarta na kowane dan wasan Afirka. Samy Morsy na Ipswich Town da kasar Masar, shi ne ya fi kowanne dan Afirka samun katin gargadi (10), sai Gueye da Semenyo da ke da 9 kowanne. An kwace kwallo daga kafar Mohammed Kudus na Ghana da West Ham sau 93, sannan ya buga kwallon da ta daki turke sau shida. Salah da Jackson da Palmer ne kawai suka zarta shi.

Danwasan gaban Chelsea da Senegal Jackson ya yi satar gida fiye da kowa har sau 23. Chris Wood, da Dominic Calbert-Lewin, da Jamie Bardy ne kadai suka kara shi.

Shi kuma dan wasa Taiwo Awoniyi ya fi kowanne dan kwallon Afirka shiga wasa daga baya a Forest, inda Jack Taylor na Ipswich ne kawai ya dara shi zama a bencin. Wasa 23 cikin 26 da dan Najeriyar ya buga ya shiga ne bayan fara wasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Basaraken Da Aka Sace A Kogi Ya Kuɓuta Bayan Shafe Kwanaki 27 A Hannun ‘Yan Bindiga