Muna samun galabar daƙile kwararowar baƙin haure — Jamus
Published: 2nd, April 2025 GMT
Gwamnatin Jamus ta ce tana ci gaba da samun galaba na daƙile kwararar baƙin haure masu shiga ƙasar tare da mayar da wadanda aka yi watsi da takardunsu na neman mafaka zuwa inda suka fito.
Ministar harkokin cikin gida ta Jamus, Nancy Faeser, ta bayyana cewa gwamnatin ƙasar mai barin gado ta taka muhimmiyar rawa wajen daƙile shigar baƙin haure cikin ƙasar.
Faeser ta ce gwamnatin na ci gaba da daukan matakin mayar da baƙin haure ƙasashen da suka fito, inda yanzu haka aka samu raguwar masu ajiye takardun neman mafaka a ƙasar, mafi ƙarfin tattalin arziki tsakanin ƙasashen Turai.
Faeser ta ce gwamnatin da Olaf Scholz ke jagoranta ta aiwatar da manufofi masu tasiri da suka taimaka wajen daƙile shigar baƙin haure zuwa ƙasar Jamus.
Nancy Faeser ’yar jam’iyyar SPD mai mulki za ta ajiye muƙamin na ministar cikin gida da zarar an kafa sabuwar gwamnati, bayan zaɓen da jam’iyyar CDU ta kasance a matsayi na farko wanda aka yi ranar 23 ga watan Fabrairun wannan shekara ta 2025.
Ana sa ran Friedrich Merz na jam’iyyar CDU ya zama shugaban gwamnatin na gaba da za a kafa a ƙasar ta Jamus.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
A shekara ta 2009, hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya ta dauki Yusuf aiki a matsayin mataimakin koci ga Samson Siasia wanda ke rike da mukamin babban kocin tawagar kwallon kafa ta Nijeriya, Yusuf har yanzu yana aiki da Siasia, ya taimakawa Pillars samun gurbin shiga gasar cin kofin CAF, a shekarar 2012 ya koma Enyimba inda ya maye gurbin Austin Eguavoen a matsayin koci kuma ya taimaka masu wajen lashe kofin gasar Federation Cup na shekarar 2013.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp