Aminiya:
2025-06-15@19:00:58 GMT

Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano

Published: 30th, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Kano, ta kama wani matashi bisa zargin kashe jami’in tsaron sa-kai a filin Idi yayin hawan sallah ƙarama.

A cewar sanarwar da ’yan sanda suka fitar, matashin mai shekara 20, ya daɓa wa jami’in wuƙa yayin da yake aiki tare da tawagar Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, bayan sallar Idi a ranar Lahadi.

Farashin fetur ya ƙaru sakamakon hana Dangote mai a Naira Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi

Haka kuma, wani jami’in sa-kai ma ya ji rauni kuma yana jinya a Asibitin Murtala Muhammad da ke Kano.

Rundunar ’yan sandan ta ce ta fara bincike kan lamarin, kuma ta gayyaci Shamakin Kano, Alhaji Wada Isyaku, domin amsa tambayoyi.

A baya-bayan nan, ’yan sanda sun hana gudanar da Hawan Sallah a Kano, yayin da ake ci gaba da rikicin sarauta tsakanin Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Sallah Sarkin Sanusi II

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi

A cewarsa, dukkanin takardar neman kirkirar sabon masarauta ko sarki ko gunduma dole ne a aike zuwa addireshin gwamnan jihar ta hannun babbar sakatariyar ma’aikatar kananan hukumomi da kula da masarautu na jihar.

Kazalika, ya ce dole ne masu nema su gabatar da takaitaccen tarihin al’ummar da suke nema wa masarauta ko sarki ko gudunmawa tare da tarihin masarautar ko sarki ko gundumar da ke yankin da suke neman fita daga ciki.

Sanarwar ta kuma nemi a sanya dukkanin wani muhimmin bayanin da aka san zai iya taimakawa wajen la’akari da bukatar masu nema.

Har ila yau, sanarwar ta ce dole ne a takardar neman a samu sahihin sanya hannun hakimi, sarakunam kauye, da shugabannin al’umma tare da tabbacin wannan neman ta fito ne daga al’ummar wannan yankin da ake nema mata masarauta ko sarki ko gunduma.

Sanarwar ta kara da cewa duk al’ummomin da ke son kirkirar sabbin masarautu, sarakuna, ko gundumomi su na da dama kuma su na da ‘yancin gabatar da bukatar neman.

Gidado ya jaddada cewa shirin na daya daga cikin kudirin gwamnati na bunkasa gudanar da harkokin kananan hukumomi, da kiyaye al’adu, da karfafa cibiyoyin gargajiya a matsayin muhimman ginshikan zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba masu ma’ana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara