HausaTv:
2025-08-02@00:07:01 GMT

Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen A Daren Jiya

Published: 31st, March 2025 GMT

Jiragen yakin Amurka sun kai sabbin hare-hare kan kasar Yemen a daren Lahadi a wasu yankuna a birnin San’aa babban birnin kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bada sanarwan cewa a safiyar yau Litinin ne jiragen yakin Amurkan suka kai hare-hare har  13 a kan wurare daban-daban a kasar, daga ciki har da Yankunan  Malikah da Sarf na birnin San’aa babban birnin kasar.

Wasu kafafen yada labaran kasar Yemen sun bayyana cewa, kafin haka jiragen yakin Amurka sun kai hare-hare a kan kasar ta Yemen wadanda suka kai ga shahadar fararen hula 12 da kuma raunata wasu 2 a birnin San’aa babban birnin kasar.

Washington ta bada sanarwan cewa ta na kai hare-haren don tabbatar da tsaron jiragen ruwan kasuwanci da suke wucewa a tekun red Sea. Alhali gwamnatin kasar Yemen ta ce tana kai hare-hare kan jiragen ruwan HKI ko masu zuwa HKI ne kawai. Sauran jiragen ruwan kasuwanci suna wucewa ba tare da wata matsala ba.

Banda haka sojojin kasar Yemen sun maida martanin hare-haren da Amurka take kaiwa kan kasar, tare da cilla makamai masu linzami kan jiragen yakin Amurka da na HKI a tekun re sea da kuma tashar jiragen sama ta Bengerion a HKI.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jiragen yakin Amurka kai hare hare kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar

Kamfanin dillancin labarun ” Mehr” ya bayyana cewa; Ziyarar da shugaban kasar ta Iran zai kai zuwa Pakistan amsa karan Fira minister Shahbaz Sharif ne.

Bugu da kari ziyarar za a yi ta ne a daidai lokacin da wannan yankin yake fama da sauye-sauye, haka nan kuma za ta mayar da hankali wajen bunkasa alakar kasashen biyu.

Majiyar kasashen biyu, Iran da Pakistan sun ce shugaban kasar ta Iran Mas’ud Fizishkiyan zai fara ziyarar tashi daga birnin Lahor ne, inda zai ziyarci hubbaren shahararren masanin kasar Allamha Muhammad Iqbal, sannan ya nufi binrin Islamaabab domin ganawa da jmai’an gwamnatin kasar.Daga cikin wadanda zai gana da su a can babban birnin kasar da akwai ‘yan siyasa da kuma jami’an soja da su ka hada da shugaban kasa Ali Zardari da Fira minister Shahbaz Sharif.

Bugu da kari shugaban kasar ta Iran zai gana da masanan kasar ta Pakistan  da kuma ‘yan kasuwa domin bunkasa alakar tattalinn arziki da alakar al’adu da addini a tsakanin kasashen biyu.

Ta fuskar kasuwancin kuwa,kasashen biyu suna son ganin an kara yawan musayar haja a tsakaninsu domin ta haura dala biliyan 3.

Wannan dai ita ce Ziyara ta biyu da shugaban kasar Iran zai kai kasar Pakistan a cikin shekaru biyu. A cikin watan Aprilu 2024, shugaban kasar  Iran shahida Ibrahim Ra’isi  ya ziyarci Pakistan.

Watanni  biyu da su ka gabata Fira Ministan kasar ta Pakistan Shahbaz Sharif ya kawo Ziyara Iran.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya August 1, 2025 Sayyid Abdulmalik Husi: Taimakon Da Ake Jefawa Gaza Ta Sama Yaudara Ce August 1, 2025 Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka July 31, 2025 Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu July 31, 2025 Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara July 31, 2025 Canada Zata Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu A Taron MDD July 31, 2025  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI July 31, 2025  Sojojin Mamaya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza July 31, 2025 Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki July 31, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
  • Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
  • Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
  • Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar
  • Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka