HausaTv:
2025-11-03@04:04:45 GMT

Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen A Daren Jiya

Published: 31st, March 2025 GMT

Jiragen yakin Amurka sun kai sabbin hare-hare kan kasar Yemen a daren Lahadi a wasu yankuna a birnin San’aa babban birnin kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bada sanarwan cewa a safiyar yau Litinin ne jiragen yakin Amurkan suka kai hare-hare har  13 a kan wurare daban-daban a kasar, daga ciki har da Yankunan  Malikah da Sarf na birnin San’aa babban birnin kasar.

Wasu kafafen yada labaran kasar Yemen sun bayyana cewa, kafin haka jiragen yakin Amurka sun kai hare-hare a kan kasar ta Yemen wadanda suka kai ga shahadar fararen hula 12 da kuma raunata wasu 2 a birnin San’aa babban birnin kasar.

Washington ta bada sanarwan cewa ta na kai hare-haren don tabbatar da tsaron jiragen ruwan kasuwanci da suke wucewa a tekun red Sea. Alhali gwamnatin kasar Yemen ta ce tana kai hare-hare kan jiragen ruwan HKI ko masu zuwa HKI ne kawai. Sauran jiragen ruwan kasuwanci suna wucewa ba tare da wata matsala ba.

Banda haka sojojin kasar Yemen sun maida martanin hare-haren da Amurka take kaiwa kan kasar, tare da cilla makamai masu linzami kan jiragen yakin Amurka da na HKI a tekun re sea da kuma tashar jiragen sama ta Bengerion a HKI.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jiragen yakin Amurka kai hare hare kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania

Hukumar kare hakkin bil’adam dake karkashin MDD ya sanar da cewa tana sa ido akan kashe-kashe da rashin adalcin da ake yi a karkashin zaben shugaban kas ana kasar Tanzania. Tun a ranar Larabar da ta gabata ne dai da ake zaben rikici ya barke a kasar sabod kin amincewar ‘yan hamayya akan yadda zaben zai gudana ba tare da manyan ‘yan takara ba. Shugabar kasar Samia Suluhu Hassan ce dai babbar ‘yar takara. Babbar jam’iyyar adawa ta sanar da cewa fiye da mutane 700 ne aka kashe a fadin kasar da ake Zanga-zanga. Shugaban ofishin hukumar kare hakkin bil’adama na MDD Seif Magango ya sanar da cewa; Sun karbi rahoranni daga majiya mai tush akan cewa a kalla an kashe mutane 10. Hukumar ta yi kira ga jami’an tsaron kasar ta Tanzania da su daina amfani da karfi a inda bai dace ba, daga cikin har da amfani da makamai akan masu Zanga-zanga. Haka nan kuma sun yi kira ga masu Zanga-zanga da su yi a cikin ruwan sanyi. Ita kuwa kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta ce nata rahoton ya tabbatar mata da cewa an kashe abinda bai kasa mutane 100 ba. Tuni dai aka kafa dokar ta baci da hana zirga-zarga a babban birnin ksar Darus-salam, ana kuma rufe hanyoyin sadarwa na interten daga lokaci zuwa lokaci. Har ila yau MDD  tana yin kira da a saki dukkanin wadanda ake tsare da su.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa