Kungiyar bada agaji ta RED CROSS ta yi allawadai da HKI saboda kissan likitoci 8 a garin Rafah na kudancin gaza a ranar 23 ga watan Maris da muke ciki.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar tana fadar haka a jiya lahadi bayanda aka basu daman dauko gawakin likitocin wadanda suka rasa rayukansu a cikin watan Motar amblance ta daular marasa lafiya.

Labarin ya bayyana cewa lokitocin suna kan hanyarsu ta zuwa unguwar Hashasha inda HKI ta kai hare-hare kan Falasdinawa don basu taimakon gaggawa.

Banda haka sai da aka dauki mako guda cur da kashe likitocin kafin sojojin yahudawan su bada damar a dauki gawakin nasu.

Ya zuwa yanzu dai tun bayan fara yakin Tufanul Aksa falasdinawa dubu 50 da kari ne sojojin HKI suka kashe a gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Leroy Sane ya koma Galatasaray

Kungiyar kwallon kafa ta Galatasaray a wannan Alhamis din ta sanar da daukar dan wasan Jamus, Leroy Sane daga Bayern Munich.

Kungiyar ta Turkiyya ta dauki dan wasan ne kyauta bayan kwantaraginsa ya kare a Munich.

Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane

Sane mai shekaru 29 ya rattaba hannu kan kwantaragin shekaru uku inda zai rika daukar albashin Yuro miliyan 9 — kwantankwacin Dala miliyan 10.4 — duk shekara kamar yadda kulob din bayyana.

Sane ya buga wa kasarsa ta Jamus wasanni 70, inda kuma ya lashe kofunan Bundesliga guda hudu a Bayern Munich tun bayan raba gari da Manchester City, inda ya dauki Firimiyar Ingila guda biyu.

A kakar bana Sane ya jefa kwallaye 13 a duk gasannin da ya haska, inda ya taimaka wa Bayern lashe gasar Bundesliga bayan ta subuce daga hannunta a kakar bara.

 

AFP

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu