Aminiya:
2025-06-21@12:55:57 GMT

Inter Milan ta koro Barcelona daga Gasar Zakarun Turai

Published: 7th, May 2025 GMT

Inter Milan ta samu nasarar tankaɗo Barcelona daga Gasar Zakarun Turai, lamarin da ya ba ta damar kaiwa zagayen ƙarshe na gasar ta bana.

A daren wannan Talatar ce aka buga wasa falle na biyu a zagayen kusa da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai ta bana tsakanin ƙungiyoyin biyu.

‘Raini ne ya sa ake ƙalubalantar yunƙurin kafa ƙungiyar Hausawa zalla’ Majalisar Dattawa ta kafa kwamitin lura da gwamnan riƙo na Jihar Ribas

Inter Milan ce ta yi nasarar doke Barcelona da ci 4-3 a filin wasanta na San Siro da ke Italiya, bayan a makon jiya sun yi kunnen doki 3-3 a Nou Camp da ke ƙasar Sifaniya.

A wasan na yau da aka barje gumi har tsawon mintuna 120, Lautaro Martinez da Hakan Calhanoglu ne suka fara ci wa Inter ƙwallo a ragar Barcelona, daga baya Eric Garcia da Dani Olmo da Raphinha suka rama ƙwallayen har da ƙari.

Sai dai ana dab da tashi ne kuma Francesco Acerbi mai shekaru 37 ya rama wa Inter ƙwallo ta uku, abin da ya tilasta wasan zuwa ƙarin lokaci.

A minti na 99 ne Davide Frattesi ya ci wa Inter Milan ƙwallon da ya ba ta nasara.

Ƙungiyar wadda a yanzu Simone Inzaghi ke jagoranta, ta kai wasan ƙarshe na Gasar Zakarun Turai karo na biyu ke nan a cikin shekaru uku.

Yanzu Inter Milan za ta haɗu ne da PSG ko Arsenal waɗanda za su fafata nasu wasan a ranar Laraba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barcelona Gasar Zakarun Turai a Gasar Zakarun Turai

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Yan Najeriya da dama ne dai da suka yi ilimin zamani dole ta sa suka rungumi sana’o’in da a baya ake ganin na kaskantattu ne don su samu na sakawa a bakin salati.

Mai yiwuwa hakan ne ya sa wasu, musamman matasa, suka yanke kauna da cewa shafe lokaci ana karatun kan iya taimaka wa mutum magance bukatunsa nay au da kullum.

NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?

Wannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
  • GORON JUMA’A 20-06-2025
  • Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya
  • Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal
  • Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba