Babbar Kotun Shari’a ta Minna a Jihar Neja ta bayar da wani umarnin na wucin gadi game da gidan rediyon Badeggi Radio Broadcasting Services Ltd, inda ta hana Gwamnatin Jihar  ɗaukar duk wata matsaya da za ta dakatar da ayyukan gidan rediyon.

Mai Shari’a Mohammed Mohammed ne ya yanke hukuncin bisa ƙorafin gaggawa (motion ex-parte) da Badeggi Radio Broadcasting Services Ltd da Daraktan gudanarwarta, Mohammed Shuaibu Badeggi, suka gabatar a kotun da ke Minna.

A cikin ƙorafin, lauyoyin masu ƙara sun jingina hujjoji da sassa daban-daban na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na shekarar 1999 (wanda aka yi wa gyara), da kuma Dokar Hukumar Kula da Watsa Labarai ta Ƙasa (NBC Act).

Hukuncin kotun ya hana wadanda ake ƙara, ciki har da Gwamnan Jihar Neja, Antoni Janar da Kwamishinan Shari’a, da Hukumar Raya Birane ta Jihar Neja, daukar duk wani mataki da zai kawo cikas ga lasisin watsa shirye-shirye ko ayyukan kasuwancin kamfanin dake cikin harabar gidan talabijin na N.T.A a Uphill, Minna.

A yayin yanke hukuncin, Mai Shari’a Mohammed Mohammed ya ce yana da matuƙar muhimmanci a bar komai yadda yake (status quo) har sai an kammala sauraron babbar ƙarar gaba ɗaya.

Umarnin na wucin gadi ya haramta ayyuka kamar soke lasisi, janye lasisi, kwacewa, ko kai farmaki da rushe wurin da kamfanin ke gudanar da ayyukansa.

Lauyan masu ƙara, Barista Philip Emmanuel, ya bayyana jin daɗinsa da hukuncin kotun, yana mai cewa hakan babbar nasara ce wajen kare haƙƙin abokan aikinsa.

An shirya cigaba da sauraron ƙarar a wani lokaci domin zurfafa bincike kan batutuwan da ke gaban kotu.

 

Daga Aliyu Lawal

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Spain za ta hada kai da kotun ICC domin gudanar da bincike kan laifukan da Isra’ila ta aikata a Gaza

Tsarin shari’a na kasar Spain zai hada kai da kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa da kotun duniya domin binciken laifukan yaki da Isra’ila ta aikata a zirin Gaza.”

Wannan yunkurin “ya mayar da martani ga shawarar rahoton kwamitin bincike na Majalisar Ɗinkin Duniya mai zaman kansa (IOC) kan yankin Falasɗinawa da aka mamaye, wanda ya bukaci bangarorin Amurka su ba da hadin kai ga binciken da ofishin mai shigar da kara na kotunan manyan laifuka ta kasa da kasa.”

Za a sanar da sakamakon binciken ga kotun kasa da kasa da kuma ofishin mai gabatar da kara na kotun hukunta manyan laifuka ta duniya.

ministan harkokin cikin gida na Spain, Fernando Grande-Marlaska, ya goyi bayan matakin shari’ar na Spain, yana ganin ya na da”ma’ana” da kuma ya zama “wajibi” don bincikin laifuffukan da aka aikata a Gaza ta fuskar “kisan kare dangi”.

Kasar Spain ta nuna goyon bayanta ga al’ummar Palastinu, inda aka gudanar da gagarumin zanga-zanga a birnin Madrid da wasu garuruwa domin yin tir da yakin kisan kare dangi da Isra’ila ke yi a Gaza.

Har ila yau kasar na cikin wadanda suka shiga shari’ar da Afirka ta Kudu ta fara a gaban kotun kasa da kasa, tana zargin Isra’ila da aikata kisan kiyashi a zirin Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Falasdinawa 47 sun yi shahada a Hare-haren Isra’ila September 20, 2025 Sudan: Rundunar Daukin Gaggawa ( R.S.F ) Ta Kashe Mutane 75 A Wani Hari Da Ta Kai Wa Masallaci A Garin Al-Fasha September 20, 2025 Pakistan: Makaman Nukiliyarmu Suna Cikin Yarjejeniyar Tsaro Da Mu Ka Kulla Da Saudiyya September 20, 2025 Adadin Falasdinawa Da HKI Ta Kashe Da Jikkatawa Sun Haura 230,000 September 20, 2025  Sheikh Na’im Kassim Ya Kira Yi Saudiyya Da Ta  Bude Sabon Shafi Da Gwagwarmaya September 20, 2025 Arqchi: Iran Ba Ta Amince Da Duk Wani Matakin Matsin Lamba Da Rashin Adalci Ba September 20, 2025 Jakadan Iran A MDDuniya Ya Ce: Kwamitin Sulhu Ya Rasa Damar Tattaunawa Da Fahimtar Juna September 20, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Jaddada ‘Yancin Kasar Na Mayar Da Martani Kan Sabawa Doka September 20, 2025 Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Mayar Da Martani Kan Zargin Shugaban Kasar Faransa September 20, 2025 Shugaban Kasar Faransa Zai Amince Da Kasar Falasdinu A Ranar Litinin Mai Zuwa A Birnin New York September 20, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Spain za ta hada kai da kotun ICC domin gudanar da bincike kan laifukan da Isra’ila ta aikata a Gaza
  • Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Sauya Sunan Ma’aikatar Mata
  • Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
  • Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
  • An yanke wa Soja hukuncin kisa ta hanyar rataya
  • Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar
  • Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja
  • SEMA Jigawa Da NEMA Da UNICEF Sun Bada Horo Akan Agajin Gaggawa A Auyo
  • ’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja