Babbar Kotun Shari’a ta Minna a Jihar Neja ta bayar da wani umarnin na wucin gadi game da gidan rediyon Badeggi Radio Broadcasting Services Ltd, inda ta hana Gwamnatin Jihar  ɗaukar duk wata matsaya da za ta dakatar da ayyukan gidan rediyon.

Mai Shari’a Mohammed Mohammed ne ya yanke hukuncin bisa ƙorafin gaggawa (motion ex-parte) da Badeggi Radio Broadcasting Services Ltd da Daraktan gudanarwarta, Mohammed Shuaibu Badeggi, suka gabatar a kotun da ke Minna.

A cikin ƙorafin, lauyoyin masu ƙara sun jingina hujjoji da sassa daban-daban na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na shekarar 1999 (wanda aka yi wa gyara), da kuma Dokar Hukumar Kula da Watsa Labarai ta Ƙasa (NBC Act).

Hukuncin kotun ya hana wadanda ake ƙara, ciki har da Gwamnan Jihar Neja, Antoni Janar da Kwamishinan Shari’a, da Hukumar Raya Birane ta Jihar Neja, daukar duk wani mataki da zai kawo cikas ga lasisin watsa shirye-shirye ko ayyukan kasuwancin kamfanin dake cikin harabar gidan talabijin na N.T.A a Uphill, Minna.

A yayin yanke hukuncin, Mai Shari’a Mohammed Mohammed ya ce yana da matuƙar muhimmanci a bar komai yadda yake (status quo) har sai an kammala sauraron babbar ƙarar gaba ɗaya.

Umarnin na wucin gadi ya haramta ayyuka kamar soke lasisi, janye lasisi, kwacewa, ko kai farmaki da rushe wurin da kamfanin ke gudanar da ayyukansa.

Lauyan masu ƙara, Barista Philip Emmanuel, ya bayyana jin daɗinsa da hukuncin kotun, yana mai cewa hakan babbar nasara ce wajen kare haƙƙin abokan aikinsa.

An shirya cigaba da sauraron ƙarar a wani lokaci domin zurfafa bincike kan batutuwan da ke gaban kotu.

 

Daga Aliyu Lawal

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Raba takardun daukar Aiki Ga Sabbin Ma’aikatan Gona Su 1 ,038

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya raba wa sabbin ma’aikatan aikin gona 1,038 da aka dauka aiki takardun su na kama aiki.

 

Bikin, ya gudana ne a gidan gwamnatin Kano.

 

Da yake jawabi yayin bikin gwamnan ya gargade su da su guji cin hanci da rashawa, ya kuma bukace su da su yi wa jihar hidima cikin himma da gaskiya.

 

 

Ya ce matakin ya nuna wani gagarumin ci gaba a kokarin da jihar ke yi na inganta samar da abinci da kuma habaka arzikin iyali.

 

 

Gwamna Yusuf ya bayyana daukar ma’aikata a matsayin cika alkawuran da ya dauka a lokacin yakin neman zabe da kuma wani muhimmin mataki na cimma wadannan manufofin.

 

“Yau rana ce ta sabuwar dama da cika alkawarin da muka dauka a yakin neman zabe, wadannan ayyuka ba wai kawai za su tallafa wajen samar da abinci ba, har ma da samar da kudaden shiga ga dubban iyalan Kano.”

 

Gwamnan ya bayyana cewa, duk da cewa Kano ta riga ta jagoranci kasar nan wajen yawan ma’aikata, amma duk da haka jihar na bukatar karin biyan bukatun noma na zamani.

 

 

“Muna bukatar karin kwararrun ma’aikatan da za su yi wa al’ummominsu hidima, da tallafa wa manomanmu, da kuma taimakawa wajen kawo sauyi a fannin noma.”

 

Gwamna Yusuf ya gargadi sabbin ma’aikatan da su guji cin hanci da rashawa, rashin zuwa aiki, da rashin tausayi, yana mai jaddada cewa daukar ma’aikata ba wata hanya ce ta wawure dukiyar al’umma ba.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru
  • ’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu
  • LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya
  • Gobara ta cinye gidan hakimi a Bauchi
  • Gwamna Yusuf Ya Raba takardun daukar Aiki Ga Sabbin Ma’aikatan Gona Su 1 ,038
  • Za a mayar da gidan yarin da ya haura shekara 100 zuwa gidan tarihi a Kano
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi
  • Kano Za Ta Mayar Da Gidan Yarin Kurmawa Zuwa Gidan Tarihi – Gwamnati