Jami’an Alhazai na shiyya-shiyya sun karrama Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa nasarorin da aka samu a aikin hajjin shekarar 2025.

 

Shugaban jami’an alhazai na shiyya-shiyya, Alhaji Sale Haruna Kafin Hausa ya tabbatar da hakan a wani kwarya-kwaryan biki da aka gudanar a shelkwatar hukumar dake Dutse Babban Birnin jihar.

 

Ya ce karrama Ahmed Labbo, na da nasaba da gudunmawar da ya bayar da kuma samun nasarar aikin hajjin bana a gida da kuma kasar Saudi Arabia.

 

Yace wadannan nasarorin sun sanya hukumar ta samu lambobin yabo da kyautuka da dama a kasa mai tsarki.

 

Alhaji Sale Haruna Kafin Hausa, yana mai cewar jami’an alhazai na shiyya-shiyya suna alfahari da Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa yadda yake kula da su da kuma tafiya da kowa wajen gudanar da aikin hajji.

 

Da yake maida jawabi, Darakta janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yaba ma jami’an bisa wannan karamci da kuma gode musu bisa kokarin su wajen kula da alhazai a aikin hajjin bana.

 

Shima a nasa tsokacin, Mai bai wa Gwamna Umar Namadi shawara akan aikin hajji, Alhaji Isa Idris Gwaram ya bayyana Alhaji Ahmed Umar Labbo a matsayin Shugaba abun koyi da hukumar alhazai ta jihar take alfahari da shi.

 

Wakilinmu, ya shaida mana cewar, a yayin bikin an kuma karrama Daraktan kudi da mulki na hukumar, Alhaji Jamilu Ilu Kazaure wanda ya yi ritaya daga aiki.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Karramawa Alhaji Ahmed Umar Labbo

এছাড়াও পড়ুন:

Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa

Kwamishinan lafiya na Jihar Adamawa, Dokta Felix Tangwami ya bayyana cewa, cutar kwalara a Ƙaramar hukumar Mubi ta yi sanadin mutuwar mutane 10, inda ya buƙaci mazauna yankin da su kula da tsaftar jikinsu.

Da yake yi wa Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) bayani a Yola ranar Laraba, Tangwami ya ce marasa lafiyan sun mutu ne a gida maimakon a cibiyoyin lafiya.

Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita

Ya ƙara da cewa, gwamnatin jihar tare da haɗin gwiwar hukumar lafiya ta duniya (WHO) sun ɗauki matakin gaggawa don daƙile ɓarkewar cutar.

“Tun daga farko, mun ɗauki matakin gaggawa a kan lamarin, kasancewar mu a can, kuma ba za a iya musanta hakan ba,” in ji shi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa, waɗanda suka ziyarci cibiyoyin kiwon lafiya sun samu kulawa, inda aka kwantar da majinyata 25 a ranar Talata 4 ga watan Nuwamba, yayin da wasu da dama kuma an sallame su tare da wayar da su kan harkokin tsafta.

Ya bayyana cewa, an tura jami’an kula da cututtuka na jihar, da Daraktan kula da cututtuka a Hukumar kula da kiwon lafiya a matakin farko, da masu aikin sa-kai zuwa Mubi domin gudanar da ayyuka da kuma wayar da kan jama’a.

Sun kuma gano waɗanda abin ya shafa a cikin unguwanni don tabbatar da sun samu kulawar lafiya.

Tangwami ya kuma yi kira ga shugabannin gargajiya da su goyi bayan ƙoƙarin gwamnati ta hanyar ƙarfafa gwiwar mazauna yankin da su gaggauta neman magani a cibiyoyin lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya
  • CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST
  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano
  • Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i