Jami’an Alhazai na shiyya-shiyya sun karrama Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa nasarorin da aka samu a aikin hajjin shekarar 2025.

 

Shugaban jami’an alhazai na shiyya-shiyya, Alhaji Sale Haruna Kafin Hausa ya tabbatar da hakan a wani kwarya-kwaryan biki da aka gudanar a shelkwatar hukumar dake Dutse Babban Birnin jihar.

 

Ya ce karrama Ahmed Labbo, na da nasaba da gudunmawar da ya bayar da kuma samun nasarar aikin hajjin bana a gida da kuma kasar Saudi Arabia.

 

Yace wadannan nasarorin sun sanya hukumar ta samu lambobin yabo da kyautuka da dama a kasa mai tsarki.

 

Alhaji Sale Haruna Kafin Hausa, yana mai cewar jami’an alhazai na shiyya-shiyya suna alfahari da Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa yadda yake kula da su da kuma tafiya da kowa wajen gudanar da aikin hajji.

 

Da yake maida jawabi, Darakta janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yaba ma jami’an bisa wannan karamci da kuma gode musu bisa kokarin su wajen kula da alhazai a aikin hajjin bana.

 

Shima a nasa tsokacin, Mai bai wa Gwamna Umar Namadi shawara akan aikin hajji, Alhaji Isa Idris Gwaram ya bayyana Alhaji Ahmed Umar Labbo a matsayin Shugaba abun koyi da hukumar alhazai ta jihar take alfahari da shi.

 

Wakilinmu, ya shaida mana cewar, a yayin bikin an kuma karrama Daraktan kudi da mulki na hukumar, Alhaji Jamilu Ilu Kazaure wanda ya yi ritaya daga aiki.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Karramawa Alhaji Ahmed Umar Labbo

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Ta Dauki Manyan Matakan Kare Jihar Daga Ambaliyar Ruwa

Gwamnatin Jihar Jigawa ta sake jaddada kudirin ta na kare al’umma daga ambaliyar ruwa kamar yadda hukumar hasashen yanayi ta kasa ta yi hasashen samu a wasu kananan hukumomin jihar a daminar bana.

Mataimakin Shugaban kwamitin fasaha kan magance ambaliya, kuma mai bai wa Gwamna Umar Namadi shawara kan ambaliya da kuma sauyin yanayi, Alhaji Hamza Muhammad Hadejia ya bayyana haka yayin da yake duba aikin jingar ruwan kogi da ya ratsa garuruwan Auyo da Tsidir da Agin da Matsa da Sorakin da Jiyan da Tage da Turabu da kuma Tandanu.

Alhaji Hamza Hadejia ya ce daga zuwan Gwamna Umar Namadi kan karagar mulkin Jihar, ya dauki kwararan matakai don kaucewa ambaliyar ruwa, domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ya kuma bayyana cewar, Gwamna Namadi ya inganta harkar noma don tabbatar da isasshen abinci da samar da ayyukan yi ga al’ummar karkara.

A cewar sa, kwamitin fasaha na magance ambaliya ya zage damtse wajen sarrafa koguna da gina kwarya-kwaryar shinge a wuraren da ake sa ran ambaliya domin magance matsalar.

A don haka, Hamza Muhammad Hadejia, ya bukaci jama’a su ci gaba da bada hadin kai da goyon baya ga gwamnatin jihar domin a cimma wannan manufa domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

ya kuma yabawa Gwamna Umar Namadi bisa hadin kai da goyon bayan da ya ke baiwa ayyukan kwamitin a kowane lokaci.

A jawaban su, Dagacin Turabu Malam Shu’aibu Saje da Shugaban ci gaban al’umma Sani Barde da tsohon kansila Umar Jiyan, sun jinjinawa Gwamna Umar Namadi da shugaban karamar hukumar Auyo da mai ba da shawara Hamza Hadejia bisa kokarin kare rayuka da dukiyoyin su, tare da tabbatar da gudunmawar su don cimma burin gwamnati kan magance ambaliya a yankin.

Sun kuma godewa gwamnatin jihar Jigawan da ta kananan hukumomi bisa samar da ababen more rayuwa da kuma bunkasa harkokin ilimi da lafiya da ruwa da wuta da hanyoyi da kuma bunkasa noma don samar da isasshen abinci da ayyykan yi a tsakanin al’ummomin karkara.

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Malaman Jami’o’in Isra’ila Sun Nemi Jamus Ta Tilasta Dakatar Da Yakin Gaza
  • Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025
  • An soka wa jami’in Sibil Difens wuka har lahira a Jigawa
  • Burtaniya Zata Fara maida yan Gudun Hijira Zuwa Faransa Bisa Wata Sabuwar Yarjeniya
  • An Kaddamar Da Shirin Dashen Itatuwan Dabino Miliyan 50 A Jigawa
  • Gwamnatin Kano Ta Karɓi Rahoton Binciken Kwamishinan Sufuri Kan Belin Wanda Ake Zargi Da Safarar Kwayoyi
  • Gwamnan Neja Ya Bada Umarnin Sake Bude Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai.
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Kai Ziyara Ta Ta’aziyya Ga Sabon Sarkin Gusau
  • Gwamnatin Jigawa Ta Dauki Manyan Matakan Kare Jihar Daga Ambaliyar Ruwa