Matar Shugaban Karamar Hukumar Giwa, Hajiya Hadiza Ahmad Sama’ila Yakawada, ta kaddamar da Makon Shayar da Nono na Duniya na bana, tare da kira ga iyaye mata da mazajensu da su ba wa jarirai nono kacokam na tsawon watanni shida na farko.

A yayin kaddamarwar, Hajiya Hadiza ta bayyana cewa shayar da jarirai nono na da muhimmanci matuƙa wajen tabbatar da lafiyar yara da kuma inganta cigaban su tun daga ƙuruciya.

Ta kuma bayyana cewa makon yana da nufin wayar da kan jama’a musamman a tsakanin iyalai game da amfani da shayar da nono, tare da ƙarfafa gwiwar ma’aikatan lafiya da su ci gaba da fafutukar wayar da kai a fadin karamar hukumar.

A nata jawabin, Sakatariyar Lafiya ta Karamar Hukumar Giwa, Hajiya Salamatu Balarabe, wadda ta sami wakilcin Hajiya Talatu Bello, jami’ar kula da magunguna masu muhimmanci ta karamar hukumar, ta yabawa kokarin shugaban karamar hukumar, Alhaji Ahmad Sama’ila Yakawada, wajen ɗaukar matakai don tabbatar da ingantaccen kula da lafiya ga al’ummar yankin.

Ta ce karamar hukumar za ta ci gaba da himma wajen kyautata lafiyar uwa da yara a fadin Giwa.

COV/Magaji Yakawada 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Giwa LG Kaddamarwa Shayarwa karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli

Gwamnatin Jihar Kano ta sake tabbatar da kudurinta na yaki da zaizayar ƙasa, ambaliyar ruwa, da sauran matsalolin da suka shafi muhalli.

Wannan bayani ya fito ne daga Gwamna Abba Kabir Yusuf yayin kaddamar da babban shirin dashen itatuwa da za a shuka tsirrai miliyan biyar da rabi a faɗin jihar, wanda aka gudanar a ƙaramar hukumar Makoda.

Ya bayyana cewa babban burin wannan shiri shi ne magance dimbin matsalolin muhalli da ke addabar al’ummar Kano.

Gwamna Yusuf ya jaddada cewa waɗannan matsaloli sun jawo manyan kalubale ga al’umma.

Ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta samar da dukkan kayayyakin da suka wajaba don kula da tsirran da za a dasa, domin su girma yadda ya kamata tare da cika manufarsu. Wannan goyon baya na da matuƙar muhimmanci wajen nasarar shirin.

Ya bukaci dukkan shugabannin ƙananan hukumomi 44, sarakuna da jami’an raya al’umma da su shiga cikin wannan shiri, yana mai cewa halartar su na da matuƙar amfani wajen cimma burin da aka sa gaba.

“Idan aka kula da itatuwan da kyau, za su taka muhimmiyar rawa wajen rage sauyin yanayi da sauran matsalolin da suka shafi muhalli. Wannan na cikin manyan manufofin muhalli na Jihar Kano.” In ji shi.

Kwamishinan Muhalli, Dr. Dahiru Mohammad Hashim, ya yabawa Gwamna Yusuf bisa goyon bayan da yake bai wa ma’aikatar don yaki da matsalolin muhalli.

Wakilin Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammad Sanusi II, wato Sarkin Dawakin Mai Tuta Alhaji Mohammad Bello Abubakar, ya sake jaddada goyon bayan masarautar ga wannan shirin na dashen itatuwa.

A yayin taron, an gabatar da kyaututtuka ga wasu mutane da suka taka rawar gani wajen tallafawa al’ummominsu.

Wannan karramawa na matsayin kwarin gwiwa ne ga wasu domin su shiga irin waɗannan ayyuka na kula da muhalli.

 

Abdullahi Jalaluddeen

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Hadin Kai Tsakanin Cibiyoyi  Na Tabbatar Da Karfi Da Ci gaba
  • An Kaddamar Da Shirin Dashen Itatuwan Dabino Miliyan 50 A Jigawa
  • Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
  • Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa ya Samu Gagarumar Nasara a Karamar Hukumar Gwarzo
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Talauci Ke Hana Shayar Da Yara Nonon Uwa Zalla A Najeriya
  • Mai Martaba Sarkin Dutse Ya Kaddamar Da Rabon Zakka Ta Shekarar 1446