A kwanakin nan da suka gabata kuma, an kaddamar da bikin baje kolin kayayyakin masarufi na kasa da kasa karo na 5, da bikin baje kolin kayayyakin shige da fice wato Canton Fair karo na 137 a nan kasar Sin, inda yawan kamfanonin da suka halarce su suka kai matsayin koli a tarihi. Shugabar kwalejin nazarin tattalin arzikin Sin bisa salon kirkire-kirkire ta kasar Brazil madam Claudia Jannuzzi, ta ce Sin na matukar bude kofarta ga sauran sassa, tare da ba da tabbaci ga bunkasar tattalin arzikin duniya.

 

Cinikin shige da ficen Sin na samun bunkasuwa mai dorewa a gabanin duk wani kalubale. Ba shakka duniya za ta ga hakikanin halin da ake ciki, wato babu mafita a aiwatar da manufar kariyar ciniki, illa dai a bude kofa, da hadin gwiwa ta yadda za a samu ci gaba tare. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mataimakin Shugaban Majalisar Kebbi ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga

Mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kebbi, Muhammad Sama’ila Bagudo, ya kuɓuta bayan shafe fiye da mako guda a hannun ’yan bindigar da suka yi garkuwa da shi.

Aminiya ta ruwaito cewa an sace mataimakin shugaban majalisar ne a ranar Juma’a 31 ga Oktoba, 2025, jim kaɗan bayan ya kammala sallar la’asar a masallacin garinsu na Bagudo.

’Yan bindiga sun kashe kansila yayin Zaɓen Gwamnan Anambra Gwamna Soludo ya lashe Zaɓen Anambra karo na biyu

Sakataren gwamnatin jihar, Yakubu Tafida, ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin Asabar.

Bayanai sun tabbatar da cewa lamarin na zuwa ne daidai da lokacin da aka gudanar da addu’o’in haɗin kai tsakanin Musulmai da Kiristoci domin neman zaman lafiya a jihar.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar Kebbi, CSP Nafiu Abubakar, ya tabbatar da cewa an saki mataimakin shugaban majalisar.

CSP Abubakar ya bayyana cewa yanzu haka yana tare da iyalansa bayan mahukunta sun tabbatar da ƙoshin lafiyarsa a wani asibiti.

“An sace shi a ranar 31 ga Oktoba, amma an sako shi jiya [Asabar] kuma yanzu yana cikin ƙoshin lafiya kamar yadda mahukunta suka tabbatar,” in ji kakakin rundunar.

Ya ƙara da cewa rundunar ta yaba da jajircewar jami’an tsaro da suka shiga aikin ceto tare da goyon bayan al’umma, inda ya ce bayanan da jama’a suka bayar sun taka muhimmiyar rawa wajen ceto wanda aka sace lafiya.

Rundunar ta kuma tabbatar da cewa za ta ci gaba da kai hare-hare kan ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a faɗin jihar, tare da kira ga jama’a su kasance masu lura da duk wani motsi da ake zargi su kuma rika sanar da hukumomin tsaro cikin gaggawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 
  • Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo
  • An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025
  • Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa
  • CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032
  • Mataimakin Shugaban Majalisar Kebbi ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki
  • Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
  • Dan Wasan Taekwando Na Kasar Iran Abulfazl Zandi Ya Zamo Shi Ne Na Daya A Duniya
  • Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE