’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu
Published: 5th, August 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Nijeriya reshen Abuja ta sanar da cafke wasu mata ’yan gida ɗaya da ake zargi da kitsa garkuwar ƙarya da zummar karɓar kuɗin fansa na naira miliyan biyar a wurin mahaifinsu.
Kakakin rundunar, SP Josephine Adeh, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar.
Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 17 a Borno da Adamawa Buni ya shirya bikin karrama daliban da suka lashe gasar duniyaTa bayyana cewa sun samu tushen faruwar lamarin ne bayan da wani Mista Innocent, ya kai rahoton ɓacewar ’yarsa mai shekaru 16 a ranar 18 ga Yuli, 2025.
Mista Innocent ya shaida wa ’yan sandan cewa ’yar tasa ba ta dawo gida ba tun bayan da ta fita domin zana jarabawa a makarantar sakandare ta gwamnati da ke Karu.
Mahaifin ya bayyana cewa bayan wani lokaci ne wasu suka kira shi da waya suna neman kuɗin fansa kafin su saki ’yar tasa.
“Nan da nan DPO ɗin ofishin Jikwoyi ya ƙaddamar da bincike, inda aka bibiyi lambar wayar da aka kira da ita har aka gano cewa waɗanda suka kira suna zaune a wani gida a Jikwoyi Phase II,” in ji SP Adeh.
A cewarta, lokacin da aka isa gidan, an gano matashiyar da ake zargin an yi garkuwa da ita tare da wata mata a matsayin baƙuwa a gidan wani mai suna Mayowa Adedeji, suna cin abinci har da hira cikin natsuwa, babu wata alamar damuwa tattare da ita.
“Ƙarin bincike ya nuna cewa yayarta ce da saurayinta yayar suka shirya makircin, tare da haɗin gwiwar matashiyar da kanta,” in ji Adeh.
An gano cewa yayar matashiyar ta kista makircin da wani saurayinta, inda suka tsara yadda za su ɗauke ‘yar uwarta su ɓoye ta a gidan abokin saurayin, yayin da yayar za ta ci gaba da zama a gidan mahaifinsu domin nuna kamar ba ta da masaniya kan abin da ke faruwa.
“Ita kuwa matashiyar da aka ce an yi garkuwa da ita, ta amince da wannan shiri, kuma ta yarda za ta zauna a gidan yayin da mahaifinta ke cikin tashin hankali,” in ji sanarwar.
SP Adeh ta ce duka mutane huɗun da ake zargi suna hannun ‘yan sanda, inda nan gaba kaɗan a gurfanar da su a kotu da zarar an kammala cikakken bincike.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An yanke wa Soja hukuncin kisa ta hanyar rataya
Wata babbar kotun sojin Najeriya da ke zamanta a sansanin sojoji ta Maxwell Khobe da ke garin Jos a Jihar Filato ta yanke wa wani soja mai suna Lukman Musa hukuncin kisa ta hanyar rataya.
An yanke wa Musa hukuncin kisa ne a ranar Alhamis bayan da aka same shi da laifuka biyu kan kisan gilla da aka yi wa wani direban babur mai ƙafa uku mai suna Abdulrahman Isa a garin Azare na Jihar Bauchi.
Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar ’Yan sanda sun kama mutum 9 kan yin garkuwa da kansuDaily Trust ta ruwaito cewa, an fara shari’ar Musa ne a farkon watan Agustan 2025 bayan kama shi biyo bayan binciken haɗin gwiwa da jami’an sojoji sashin harkokin da hukumomin yankin suka gudanar.
Al’amarin ya ja hankalin jama’a sosai saboda tsananin mugun halin da aka aikata da kuma yunkurin tauye amanar jama’a da sojan ya yi.
Shugaban Kotun Sojojin Najeriya ta 3, Birgediya-Janar, Liafis Bello ya ce an samu sojan da laifin kisan kai da kuma mallakar harsasai ba bisa ƙa’ida ba.
Kotun ta tabbatar da cewa, shaidun da aka gabatar a lokacin shari’ar sun nuna cewa, Musa ya haɗa baki da wani mai suna Mista Oba, domin su kai Isa gidansa da zargin taimaka masa wajen kwashe kayansa.
Ya ƙara da cewa Musa ya bugi Isa a kai da wani abu na katako, inda ya sume, kafin ya shaƙe shi ya mutu.
A ƙoƙarinsu na ɓoye laifin, Musa da abokinsa sun cusa gawar wanda aka kashe a cikin buhu tare da jefa ta a tsakanin ƙauyukan Shira da Yala a Jihar Bauchi.
“An sayar da babur mai ƙafa uku na Isa daga baya, wanda ya ƙara fallasa yadda aka tsara yadda lamarin ya faru,” in ji masu gabatar da ƙara na soji yayin shari’ar.
Hakazalika sun bayyana cewa a binciken da ake yi, an samu Musa da harsashi na musamman har guda 34 na nau’in 7.62mm ba tare da wata izinin doka ba.
Da yake yanke hukuncin, Birgediya Janar Bello ya bayyana abin da Musa ya yi a matsayin “abin kunya, rashin tausayi da kuma cin zarafi da rahin a ɗa’a da kimar sojoji.”
“Ka nuna rashin tausayi daga mai kare ’yan ƙasa zuwa mai kisan gilla, matakin da kuka ɗauka abin kunya ne kuma abin kunya ga Sojojin Najeriya,” in ji kotun.