Aminiya:
2025-08-05@18:57:01 GMT

’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu

Published: 5th, August 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Nijeriya reshen Abuja ta sanar da cafke wasu mata ’yan gida ɗaya da ake zargi da kitsa garkuwar ƙarya da zummar karɓar kuɗin fansa na naira miliyan biyar a wurin mahaifinsu.

Kakakin rundunar, SP Josephine Adeh, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar.

Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 17 a Borno da Adamawa Buni ya shirya bikin karrama daliban da suka lashe gasar duniya

Ta bayyana cewa sun samu tushen faruwar lamarin ne bayan da wani Mista Innocent, ya kai rahoton ɓacewar ’yarsa mai shekaru 16 a ranar 18 ga Yuli, 2025.

Mista Innocent ya shaida wa ’yan sandan cewa ’yar tasa ba ta dawo gida ba tun bayan da ta fita domin zana jarabawa a makarantar sakandare ta gwamnati da ke Karu.

Mahaifin ya bayyana cewa bayan wani lokaci ne wasu suka kira shi da waya suna neman kuɗin fansa kafin su saki ’yar tasa.

“Nan da nan DPO ɗin ofishin Jikwoyi ya ƙaddamar da bincike, inda aka bibiyi lambar wayar da aka kira da ita har aka gano cewa waɗanda suka kira suna zaune a wani gida a Jikwoyi Phase II,” in ji SP Adeh.

A cewarta, lokacin da aka isa gidan, an gano matashiyar da ake zargin an yi garkuwa da ita tare da wata mata a matsayin baƙuwa a gidan wani mai suna Mayowa Adedeji, suna cin abinci har da hira cikin natsuwa, babu wata alamar damuwa tattare da ita.

“Ƙarin bincike ya nuna cewa yayarta ce da saurayinta yayar suka shirya makircin, tare da haɗin gwiwar matashiyar da kanta,” in ji Adeh.

An gano cewa yayar matashiyar ta kista makircin da wani saurayinta, inda suka tsara yadda za su ɗauke ‘yar uwarta su ɓoye ta a gidan abokin saurayin, yayin da yayar za ta ci gaba da zama a gidan mahaifinsu domin nuna kamar ba ta da masaniya kan abin da ke faruwa.

“Ita kuwa matashiyar da aka ce an yi garkuwa da ita, ta amince da wannan shiri, kuma ta yarda za ta zauna a gidan yayin da mahaifinta ke cikin tashin hankali,” in ji sanarwar.

SP Adeh ta ce duka mutane huɗun da ake zargi suna hannun ‘yan sanda, inda nan gaba kaɗan a gurfanar da su a kotu da zarar an kammala cikakken bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan mata Garkuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci  Sun Bayyana Cewa: Masu Shirin Halaka Gaza Suna Son Mamaye Duniyar Musulmi Ne

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun bayyana cewa: Masu shirin halaka Gaza suna neman hadiye duniyar Musulunci  ne

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci nanIran sun yi gargadin cewa; Bangarorin da ke shirya kisan kiyashi a Gaza ba wai kawai halakar al’ummar Falastinu ba ne kawai, a’a suna neman mamaye yankuna masu arziki da muhimmanci na duniyar Musulunci ne a wani bangare na ci gaba da fadada ayyukan da suka shafi tsaro da albarkatun kasa.

Dakarun kare juyin juya halin na Musuluncin sun bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Tsayin daka da gwagwarmayar da al’ummar Falastinu suke yi a yau a zirin Gaza wajen fuskantar kisan kare dangi da laifukan yahudawan sahayoniyya, wata shaida ce da ke nuni da irin sadaukarwar da wannan al’umma take da shi na ‘yantar da Falastinu da Qudus mai tsarki, da kuma ci gaba da tafarkin shahidi mai girma Isma’il Haniyyah – tsohon shugaban bangaren siyasar kungiyar Hamas da sauran shahidan ‘yar gwagwarmayar wajen fuskantar ‘yan sahayoniyya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin  Shiri August 3, 2025 Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Tana Kokarin Boye Barnarta A Zirin Gaza August 3, 2025 Tsohon Shugaban Amurka Joe Biden Ya Caccaki Trump Kan Rusa Kundin Tsarin Mulkin Kasar August 3, 2025 IRGC Tace Bata Amince Da Kasashen Biyu A Kan Kasar Falasdinu Ba August 3, 2025 Iran Da Japan Suna Iya Jagorantar Duniya Don Rabata Da Makamai Kare Dangi August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Wallafa Hotunan bidiyo Na Fursinan HKI tsare A Gaza August 3, 2025 Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62 August 3, 2025 Pezeskkian Ya Ce: Suna Fatan Musayar Kasuwancin Tsakanin Iran Da Pakistan Ta Haura Dala Biliyan 10 August 2, 2025 Araqchi: Abokantaka Da Ke Tsakanin Iran Da Pakistan Wata babbar Jari Ce Nan Gaba August 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara ta cinye gidan hakimi a Bauchi
  • Wani Dan Siyasa Ya Shirya Addu’o’i Na Musamman Domin Samun Zaman Lafiya A Zamfara
  • Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi
  • Kano Za Ta Mayar Da Gidan Yarin Kurmawa Zuwa Gidan Tarihi – Gwamnati
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci  Sun Bayyana Cewa: Masu Shirin Halaka Gaza Suna Son Mamaye Duniyar Musulmi Ne
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin  Shiri
  • Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
  • Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty
  • Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja