Manoma sun koka kan rabon takin gwamnati a Sakkwato
Published: 6th, August 2025 GMT
Manoma a Jihar Sakkwato sun koka game da takin da gwamnatin jihar ta ce za ta raba musu don noman damina cewa bai kai hannunsu ba.
Duk da cewa an ƙaddamar da rabon takin kusan mako guda da ya gabata.
Hatsarin Mota: Yadda hanyar Lambata ke laƙume rayuka a Neja Tinubu ya taya ’yan matan Yobe da suka lashe gasa a Ingila murnaGwamnan Sakkwato, Ahmed Aliyu, ya ƙaddamar da shirin sayar da takin zamani da magungunan noma a farashi mai rahusa a Ƙaramar Hukumar Gwadabawa domin bunƙasa harkar noma a daminar 2025.
Sama da buhu dubu 105 na NPK da UREA aka sayar a farashi mai rangwame.
Hakazalika, an sayi maganin kashe ƙwari da keken noma don raba wa manoma.
Sai dai manoma da dama sun ce wannan taki ba na noman damina ba ne, kuma har yanzu ba a fara rabawa ba.
Umar Yusuf, wani tsohon manomi daga Tangaza, ya ce gwamnati ta ƙaddamar da sayar da takin ne bayan damina ta kusa ƙarewa.
Kabiru Muhammad daga Kware, wanda ke da gonaki guda biyar, ya ce yana buƙatar taki amma ba a samun shi a kan lokaci.
Ya ce shirin ba ya zuwa hannun manoman gaskiya saboda ba a tsara shi yadda ya dace ba.
Muhammad Sale daga Illela ya ce ba wani manomi mai gona da ke jiran takin gwamnati, saboda duk shekara sai an makara wajen rabon taki.
Ya ce idan gwamnati ba za ta samar da taki cikin tsari ba, gara ta daina sayen shi gaba ɗaya, ta mayar da kuɗin zuwa wani aikin da zai amfani talaka da jihar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Sanarwar ta ce, “A ranar 2 ga Oktoba, 2025, misalin karfe 08:25 na safe, wani mutumin kirki ya kai rahoton kisan gilla a ofishin D Dibisional Police Headkuarters.
“Rahoton ya bayyana cewa wasu mutane biyu sun je gidan wani Ahmad Lawan, namiji, mai shekaru 29, wanda ake kira Soje, mazaunin Sabon Kasuwa, wanda ake zarginsa a matsayin shahararren dan sara-suka.”
“Suka kwankwasa kofar gidansa, bayan da ya bude, sai suka soka masa wuka a kirji sannan suka tsere zuwa wani wuri da ba a sani ba.”
Wakili ya bayyana cewa jami’an da ke karkashin D’ Dibision, karkashin jagorancin DPO CSP Mubarak Sani Baba, “sun hanzarta zuwa wurin da abin ya faru, suka dauki wanda abin ya shafa zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH), Bauchi, inda likita ya tabbatar da rasuwarsa.”
Ya kara da cewa an mika gawar ga iyalansa domin a yi masa jana’iza bisa tsarin Musulunci.
A cewar binciken farko, ‘yansanda sun gano Abubakar Ibrahim, wanda aka fi sani da Duduwa, da Abubakar Mohammed, a matsayin manyan masu hannu a kisan.
Bayan an binne Lawan, Wakil ya ce wasu fusatattun matasa sun kai farmakin ramuwar gayya inda suka kona gidan iyalin daya daga cikin wadanda ake zargi.
“Amma hadakar jami’an Rapid Response Skuad, Operation Restore Peace da D’ Dibision suka iso da gaggawa suka dakile rikicin,” in ji shi.
‘Yansanda sun kara bayyana cewa daya daga cikin manyan wadanda ake zargi, Abubakar Ibrahim (Duduwa), wanda ya fara tserewa, daga baya an gan shi yana yawo a Mararraban Liman-Katagum, kuma jami’an tsaro na sa-kai suka kama shi.
“Yayin da ake kai shi ofishin ‘yansanda, wasu fusatattun matasa suka tare su a Kwanar Kwaila suka kai masa hari da takubba, wanda ya jawo karaya a hannuwansa biyu da kuma mummunan rauni a kansa,” in ji Wakil.
Ya ce jami’an ‘yansanda sun iso da gaggawa inda suka ceci wanda ake zargin, suka tarwatsa matasan, sannan suka garzaya da shi ATBUTH domin jinya.
Sanarwar ta kara da cewa duk wadanda aka kama suna kan bincike domin tantance irin rawar da kowane dayansu ya taka a lamarin.
Wakil ya ruwaito Kwamishinan ‘Yansanda, CP Sani-Omolori Aliyu, yana gargadin iyaye da shugabannin al’umma da su ja kunnen ‘ya’yansu kada su bari a yi amfani da su wajen tayar da hankalin jama’a.
“Rundunar ba za ta yi wata-wata ba wajen daukar mataki mai tsauri kan duk wanda ko wata kungiya da gangan ta kawo tabarbarewar doka da oda ta kowace siga. Duk wanda aka kama da laifi za a hukunta shi bisa cikakkiyar doka,” in ji Aliyu.
Ya kara da cewa an tura tawagogin jami’an musamman a sassa daban-daban na jihar domin tabbatar da bin doka da oda yadda ya kamata.
A tuna cewa, kamar yadda jaridar PUNCH Metro ta ruwaito a 2024, rundunar ta taba kama wasu mutane makamantan wadannan bayan kisan gilla da aka yi wa wani Adamu Alkasim a unguwar Bayan Gari, Bauchi.
A lokacin, an kama mutum biyu Usman Shehu, mai shekara 20, da Abdullahi Abubakar, mai shekara 19, bisa zargin “hada baki wajen aikata laifi da kuma kisan kai.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA