Lauyoyin Landan suna tattara bayanai kan ‘yan Birtaniya da suka yi aiki a cikin rundunar sojojin mamayar Isra’ila

Kwararru kan harkokin shari’a na kasar Biritaniya sun ce gurfanar da wasu ‘yan kasar masu takardar ‘yan kasa biyu da ke aiki a cikin sojojin mamayar Isra’ila a gaban kuliya bisa zargin hannu a tafka laifukan yaki a Gaza, zai yi tasiri ga wadanda ke tunanin shiga cikin sahunsu.

Hakan ya biyo bayan gabatar da rahoto ga rundunar ‘yan sandan birnin Landan ne mai kunshe da shaidun da suka shafi ‘yan Birtaniya guda 10 da suka yi aikin soja karkashin rundunar mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila da ake zargi da aikata laifukan yaki a Gaza.

A cewar wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Anadolu ya wallafa, lauyoyin cibiyar kare hakkin jama’a da cibiyar kare hakkin bil’adama ta Falasdinu sun gabatar da rahoto ga sashin yaki da ta’addanci na ‘yan sandan birnin London, wanda kuma ke binciken laifukan yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ben Gafir Ya Bukaci Gwamnatin HKI Ta Mamaye Yankin Gaza Gaba daya

Ministan tsaron cikin gida na HKI Itamar Ben-Gvir ya yi kira ga babban murya kan cewa dole ne HKI ta mamaye dukka zirin gaza ta kuma kori falasdinawa da suke cikinsa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalato Ben Gafir yana fadar haka a jiya ya kuma kara da cewa mamaye gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan da kuma shi ne kawai zai sa a samar da kasar yahudawan zalla inda babu ba falasdine ko guda a yankunan guda biyu.

Kiran nasa dai ya gamu da maida martani daga yan siyasa a ciki da wajen HKI.

Tun shekara ta 2023 ne gwamnatin HKI take son mamyar zirin gaza ta kuma kori Falasdiwa a yankin. Bayan yaklin da kungiyar Hamas ta fara a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023

Amma da alamun yahudawan sun kasa, saboda har yanzunn kungiyar Hamas tan gaza kuma tana ci gaba da halaka sojojin yahudawan a cikinsa.

A halin yanzu dai yahudawan sun kashe falasdinawa fiye da dubu 50, kuma suna ci gaba da kashesu a duk ranar All.. musamman a wajen tarkon karban abinci da suka kafa masu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa Yahudawan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • Isra’ila Zata Gamu Da Maida Martani Mai Tsanani Idan Ta Kuskura Ta Sabonta Yaki Da Iran
  • Ben Gafir Ya Bukaci Gwamnatin HKI Ta Mamaye Yankin Gaza Gaba daya
  • Kalibof Yace: Iran Zata Maida Martani Mai Tsanani Kan HKI Idan Ta Sake Bude Yaki da Iran
  • Mujallar “Foreign Policy”Ta Amurka: Isra’ila Ba Ta Yi Nasara A Yaki Da Iran Ba
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Magajin Garin Birnin Tehran Ya Karyata Da’awar ‘Yan Sahayoniyya
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza