Lauyoyin Landan suna tattara bayanai kan ‘yan Birtaniya da suka yi aiki a cikin rundunar sojojin mamayar Isra’ila

Kwararru kan harkokin shari’a na kasar Biritaniya sun ce gurfanar da wasu ‘yan kasar masu takardar ‘yan kasa biyu da ke aiki a cikin sojojin mamayar Isra’ila a gaban kuliya bisa zargin hannu a tafka laifukan yaki a Gaza, zai yi tasiri ga wadanda ke tunanin shiga cikin sahunsu.

Hakan ya biyo bayan gabatar da rahoto ga rundunar ‘yan sandan birnin Landan ne mai kunshe da shaidun da suka shafi ‘yan Birtaniya guda 10 da suka yi aikin soja karkashin rundunar mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila da ake zargi da aikata laifukan yaki a Gaza.

A cewar wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Anadolu ya wallafa, lauyoyin cibiyar kare hakkin jama’a da cibiyar kare hakkin bil’adama ta Falasdinu sun gabatar da rahoto ga sashin yaki da ta’addanci na ‘yan sandan birnin London, wanda kuma ke binciken laifukan yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa

Wani dalibin shekarar ƙarshe a Jami’ar Ambrose Alli da ke jihar Edo, ya mutu a wani hatsarin mota bayan shi da wasu dalibai sun yi jerin gwanon motoci domin murnar kammala jarabawar ƙarshe.

Aminiya ta samu labari a ranar Talata daga wani mai amfani da Facebook mai suna Inside Edo, cewa hatsarin ya faru ne a ranar Litinin jim kaɗan bayan daliban sun gama jarabawar ƙarshe. Sai dai ba a bayyana sunan dalibin ba.

DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya? Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka

Majiyar ta ce motar ta yi ƙoƙarin wuce wata mota kafin ta kwace ta kuma daki wata babbar mota.

A cewar majiyar: “Wani mummunan hatsari ya faru a Ujoelen, kusa da makarantar firamare, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar wani dalibi da ya kammala karatu a jami’ar Ambrose Alli, Ekpoma.

“A cewar masu gani da ido, hatsarin ya faru ne yayin da aka yi yunƙurin wucewa da ɗaya daga cikin motocin da abin ya shafa.

“Wannan haɗarin ya jawo rasa iko, wanda ya haifar da mutuwar. Mazauna yankin da ke kusa sun ruga wurin, amma ba a iya ceto wanda ya jikkata ba.”

Haka kuma, Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa daliban sun kasance suna tukin mota cikin ganganci kafin su yi taho-mu-gama da wata babbar mota da ta tsaya a hanya.

An ce wanda ya rasu yana cikin jerin gwanon motocin da daliban da suka kammala karatu suka yi.

NAN ta ruwaito: “An ce yana cikin jerin gwanon sabbin daliban da suka shiga kan hanya a ranar Litinin jim kaɗan bayan bikin kammala makaranta.

“Lamarin ya faru ne lokacin da wanda ya rasu ya yi yunƙurin wuce wata babbar mota mai tafiya, amma ya buge da wata mota da ta tsaya a gefen hanya.”

Ƙoƙarin samun martani daga kwamandan sashe na jihar Edo a Hukumar Kiyaye Hadura ta Ƙasa (FRSC), Cyril Mathew, ya ci tura, domin lambar ba ta shiga har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

Sai dai NAN ya rawaito daga baya Mathew ya tabbatar da lamarin, yana mai cewa mutum ɗaya ya mutu yayin da wasu biyar suka jikkata a hatsarin.

Ya ce: “Daliban, bayan sun gama rubuta takardar jarabawa ta ƙarshe, sun shiga hanya cikin jerin gwanon motoci.

“A cikin wannan yanayi, ɗaya daga cikinsu ya yi yunƙurin wuce wata mota, ya kuma buge da wata babbar mota da ta tsaya a gefen hanya,” kamar yadda NAN ya rawaito daga Mathew.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
  • Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • ‘Yan Bindiga 18 Sun Muta a Wata Arangama da Rundunar Operation Fansan Yamma