Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4
Published: 6th, August 2025 GMT
’Yan bindiga sun sace mutum 150 a mabanbantan hare-haren da suka kai kauyuka daban-daban na jihar Zamfara a cikin kwana hudu.
Kakakin Gwamnatin jihar ta Zamfara, Mahmud Mohammed Dantawasa ne ya tabbatar da hakan ga BBC.
Sai dai duk da yake bai bayyana hakikanin adadin mutanen da aka sace ba, amma ya ce gwamnatinsu na iya kokarinta wajen ganin ta ceto su.
Haka na zuwa ne a daidai lokacin da malamin addinin Musuluncin nan mazaunin Kaduna, Sheikh Musa Yusuf Asadus-Sunna, ya ce kwamitin zaman lafiyar da yake jagoranta ya sami nasarar kulla yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin kasurgumin dan bindigar nan, Bello Turji, da Gwamnatin Tarayya.
Tuni dai yarjejeniyar ta kai ga sakin mutum 32 da aka yi garkuwa da su da kuma mika wasu tarin makamai ga gwamnati.
Mazauna yankunan sun ce ’yan bidnigar da ke dauke da muggan makamai ne a tsawon kwanakin suka kai hari kauyukan Sabon Garin Damri da Dakko Butsa (wanda ke da iyaka da jihar Sakkwato), da Tungar Abdu Dogo da Tungar Sarkin Daji da Sadeda da kuma kauyen Tungar Labi.
Mutanen sun ce galibi ’yan bindigar sun fi kaddamar da hare-haren ne cikin dare lokacin da mutane suke bacci, ko kuma lokacin da ake yin ruwan sama.
Kazalika, wasu majiyoyin kuma sun ce lalacewar hanyoyin jihar na taka muhimmiyar rawa wajen kara ta’azzarar hare-haren, saboda jami’an tsaro kan sha bakar wuya kafin su iya shiga yankunan su kai wa jama’a dauki cikin gaggawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun Sojin Kasar Yamen Su Kai Hare-hare A Muhimman Wurare A HKI.
Rahotanni sun bayyana cewa dakarun sojin kasar Yamen sun kaddamar da hare-hare guda 3 da gagarumar nasara a wasu mihimman wurare a HKI, da zimmar mayar da martani kan hare haren da Isra’ilan take kai mata, saboda ci gaba da nuna goyon bayan alummar falasdinu da take yi da ta kwashe shekaru biyu ta na yi musu kissan gilla,
Acikin wani bayani da kakakin sojin kasar Yamen Yahya Saree ya fitar ya sanar cewa kasarsa ta kaddamar da hare hare a muhimman wuraren guda 3 a Yaffa da HKI ta mamaye , kuma ta yi amfani da makami na haypersoni balisstic missile da ta basu suna da falasdinu na 2.
Haka zakila ta kai hari a yankin umm Rashrash wato Eilat inda ta yi amfani da jirage marasa matuki guda 3, da kuma Be’er sheva, sai dai yace za su ci gaba dakai har a Eilit ba kakkautawa. Kasar yamman ta sha alwashin ci gaba da kai hare-haren nuna goyon baya ga alummar falasdinu da ake zalunta har sai HKi ta dakatar da kisan kare dangi da take yi a gaza kuma a dauke killacewar da aka yi mata.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Isra’ila Na ci Gaba Da Kutsa Kai A Tsakiyar Gaza A Yau Juma’a September 19, 2025 Dangantaka Na Kara Tsami Tsakani Faransa Da Isra’ila Kan Amincewa Da Falasdinu . September 19, 2025 Sojojin HKI 12 Ne Suka Halaka Ko Suka Ji Rauni A Gaza September 19, 2025 Amurka Ta Yi Amfani Da Kujeran Veto Don Hana Zaman Lafiya A Gaza September 19, 2025 HKI Ta Kai Hare-Hare Kan Wurare Har 5 A Kudancin Kasar Lebanon September 19, 2025 Majiyoyin Diblomasiyya Sun Ce Washington Zata Jagoranci Turawa A Tattaunawa Da Iran September 19, 2025 Iran Ta Bukaci Kwamitin Tsaro Na MDD Ta Zabi Diblomasiyya Kan Fito Na Fito September 19, 2025 Yahudawa Suna Ci Gaba Da Yin Hijira Zuwa Wajen HKI September 18, 2025 ‘Yan Gwgawarmaya Sun Kashe Sojojin HKi 4 A Gaza September 18, 2025 An Halaka Sojojin HKI Biyu Ta Hanyar Sukarsu Da Wuka A Kusa Da Iyakar Jordan September 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci