Da safiyar Larabar nan ne kwamitin tsaron MDD ya gudanar da taron tattaunawa game da batun rikicin Isra’ila da Falasdinu, inda a jawabinsa game da aniyar Isra’ila ta tsananta hare-haren soji, da mamaye daukacin zirin Gaza, mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Geng Shuang, ya bayyana matukar damuwa kan hakan, yana mai kira ga Isra’ila da ta kauracewa wannan mataki mai hadari, yana mai fatan daukacin sassan da lamarin ya shafa za su gaggauta kaiwa ga cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta mai tsorewa.

Geng Shuang, ya kuma jaddada muhimmancin aiwatar da sahihin mataki na dakatar da bude wuta yadda ya kamata, ta yadda hakan zai kubutar da rayukan al’umma, tare da bayar da damar sakin wadanda ake tsare da su, su koma ga iyalansu. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

A yau Laraba 5 ga watan Nuwamba, an bude bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin na kasa da kasa (CIIE) karo na 8 a birnin Shanghai. A yayin wani taron manema labarai na yau da kullum da ya gudana a wannan rana, mai magana yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta nuna cewa, nasarar karbar bakuncin bikin baje kolin CIIE tsawon shekaru takwas a jere ta nuna kudurin kasar Sin da ayyukanta na cika alkawarinta na bude kofa, da kuma cimma burin samun moriyar juna da kuma nasara ga kowane bangare.

Mao Ning ta bayyana cewa bikin baje kolin na CIIE shi ne babban baje kolin kayayyaki a matakin na kasa na farko a duniya wanda ke da jigon shigo da kayayyaki daga waje, kuma wani sabon salo ne da yunkuri mai alfanu ga kasar Sin don ta fadada bude kofa ga sauran kasashe.

Girman bajen kolin CIIE na wannan shekarar ya gawurta zuwa sabon matsayi, inda kamfanoni sama da 4100 daga kasashen waje suke halarta. Harka tare da kasar Sin tamkar mabudi ne na samun damammaki, wanda hakan ya samu ittifakin amincewa a tsakanin dukkan bangarorin da suke halarta. Kasar Sin za ta ci gaba da fadada bude kofa da kuma sanya babbar kasuwarta ta zamo babbar dama ga duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka November 5, 2025 Daga Birnin Sin Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin November 5, 2025 Daga Birnin Sin Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya November 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
  • Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza
  • Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar
  • Qalibaf: Iran Da Pakistan Zasu Aiwatar Dukkan Yarjejeniyar Da Suka Cimma A Tsakaninsu
  • Kwamitin Tsaron Ya Ce: Amurka Ta Bukaci Duba Kudurin Neman Kafa Rundunar Kasa Da Kasa A Gaza
  • Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya
  • Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata
  • Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba
  • Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140