Aminiya:
2025-09-20@11:05:14 GMT

Nafisa ta cancanci kyautar Dala 100,000 da gida da OON — Pantami

Published: 5th, August 2025 GMT

Tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya ta ba wa ɗalibar nan ’yar shekara 17 daga Jihar Yobe da ta lashe Gasar Turanci ta Duniya, Nafisa Abdullah Aminu, kyautar tsabar kuɗi Dala 100,000 da gida da kuma lambar girmamawa ta OON.

Ya buƙaci a gayyato Nafisa da malamanta na harshen Turanci musamman zuwa Fadar Shugaban Ƙasa a karrama su saboda yadda suka ɗaga sunan Najeriya a idon duniya a fannin ilimi.

“Ina kira da babbar murya cewa a a ba wa Nafisa kyautar tsabar kuɗi Dala 100,000 da gida da kuma lambar girmamawa daga Gwamnatin Tarayya.”

A cikin saƙon da ya wallafa a safiyar Talata, Pantami ya ƙara da cewa malaman Nafisa sun cancanci irin kyautar da aka yi wa tawagar masu horas da ’yan wasan Najeriya ta lambar OON da tsabar kuɗi Dala 50,0000 da kuma gida ga kowannensu, musamman ma tun da nasarar da suka samu a fannin ilimi ne.

’Yar shekara 17 daga Yobe ta lashe Gasar Turanci ta Duniya Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata kyautar Dala dubu 100 da gidaje

“Su ma malananta a ba su kyauta irin wadda aka yi wa masu horas da ’yan wasan ƙwallon Najeriya. Wajibi ne mu ba wa ilimi muhimmancin da ya dace tare da karrama ƙwazon ’yan kasarmu,” in ji Pantami.

Bayanin na zuwa ne washegarin da Gwamnatin Tarayya ta yi irin wannan kyauta ga kowacce daga ’yan wasan ƙwallon kwandon Najeriya na D’Tigress kan lashe gasar Kaifin Nahiyar Afirka ta shekarar 2025.

Ƙasa da mako guda ke nan kuma bayan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi irin wannan kyauta ga ’yan wasan ƙwallon ƙafan mata ta Super Falcons bayan sun lashe gasar Kofin Nahiyar Afirka ta bana.

Aminiya ta ruwaito cewar Nafisa Abdullah Aminu ta lashe Gasar Turanci ta Duniya ta Teen Eagle da aka gudanar a ƙasar Birtaniya.

Nafisa daga Kwalejin Nigeria Tulip International (NTIC) da ke Jihar  Yobe ta doke abokan fafatawarta daga ƙasashe 69 domin zama Gwarzuwar Shekarar 2025.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gasar Turanci kyautar Dala 100 yan wasan ƙwallon

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 1,666 ne suka kashe kansu a Legas cikin shekaru biyar – ’Yan sanda

Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta ce akalla mutane 1,666 mazauna jihar Legas sun rasa ransu ta hanyoyin da ba su dace ba, ciki har da kashe kansu, tsakanin farkon 2020 zuwa karshen 2024.

Wannan bayani ya fito ne daga bakin likitan binciken gawarwaki na rundunar, ACP Samuel Keshinro, yayin gabatar da rahoton bincike kan kisan mata a wani taron da aka gudanar a jihar ranar Alhamis.

Cutar Kwalara ta kashe mutum 58 a Bauchi Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a Gaza

A cewar Keshinro, rahoton ya mayar da hankali ne kan abubuwan da suka shafi kisan kai, kashe kai, hatsarurruka da sauran hanyoyin mutuwa da ba su da alaka da cuta, domin wayar da kan jama’a da ƙarfafa fafutuka kan matsalar kisan mata.

Bayanan da aka raba a wajen taron sun nuna cewa daga cikin mutuwar 1,666, 350 mata ne, yayin da 1,306 kuma maza ne, sai mutum 10 da ba a iya tantance jinsinsu ba.

Keshinro ya ce an tattara bayanan ne domin samar da madogara mai ƙarfi wajen yanke shawara da kuma wayar da kan jama’a kan hatsarin kisan mata.

Ya ce bayanan sun nuna cewa mafi yawan kisan mata ana aikata su ne daga abokan rayuwarsu na kusa.

“Mun fito da abubuwan da muka gano ta amfani da bayanan da ke hannun ’yan sanda a ofishin CID na jihar. Mun gano cewa daga cikin mutuwar mata 350, kusan guda 70 kisan abokan zamansu ne.

“Wannan yana nuna irin raunin da mata ke ciki, musamman a inda ake tsammanin za su samu ƙauna da kariya. Kuma ya zo a daidai lokacin da Majalisar Dinkin Duniya ta ware ranar 25 ga watan Nuwamba a matsayin ranar yaki da cin zarafin mata.”

Ya kuma ba da shawarar a rungumi amfani da tsarin adana bayanai ta kwamfuta da kuma inganta hanyoyin tattara bayanai a binciken laifuka.

A nasa jawabin, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Legas, Olorundare Jimoh, ya bayyana cewa bisa ga bayanan da aka tattara cikin shekara guda, adadin kisan mata a jihar bai kai yadda ake tsammani ba idan aka kwatanta da yawan jama’ar jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gazawar Shugaba Bola Tinibu Ne Ya Sa Sanata Marafa Ficewa Daga APC
  • Takari: Rayuwar baƙin haure ’yan Najeriya mazauna Saudiyya
  • Matasan Nijeriya sun koma yin ci-rani a Nijar da Chadi
  • Mutum 1,666 ne suka kashe kansu a Legas cikin shekaru biyar – ’Yan sanda
  • Akasarin masu kai mana hare-hare daga jihohin da suka kewaye mu suke – Gwamnatin Filato
  • Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a Gaza
  • ’Yan sanda sun kama mutum 9 kan yin garkuwa da kansu
  • Juventus na son Silva, Manchester City za ta nemi Kobbie Mainoo
  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025