Aminiya:
2025-09-20@12:47:25 GMT

Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 17 a Borno da Adamawa

Published: 5th, August 2025 GMT

Dakarun sojin Nijeriya sun hallaka aƙalla ’yan ta’adda 17 na ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP a wasu hare-haren kwantan bauna da suka kai a jihohin Borno da Adamawa a tsakanin ranakun 23 ga Yuli zuwa 2 ga Agustan 2025.

Kyaftin Reuben Kovangiya, Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Sojin Kasa ta Nijeriya, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

Buni ya shirya bikin karrama daliban da suka lashe gasar duniya An soka wa jami’in Sibil Difens wuka har lahira a Jigawa

Ya bayyana cewa sojojin ƙarƙashin rundunar Operation Hadin Kai sun kai hare-haren ne a ƙananan hukumomin Bama, Konduga, Gwoza, Magumeri, da Biu a Jihar Borno, da kuma Michika da ke Jihar Adamawa.

A cewarsa, an kuma gano ababen fashewa 14 da ’yan ta’addan suka dasa a wurare daban-daban wadanda dakarun suka samu nasarar tarwatsa su.

“Ayyukan sun haifar da gagarumar nasara ga rundunar, inda muka hallaka mayaƙan, kuma muka ƙwato makamai da kayan yaƙi daban-daban da suke amfani da su wajen kai hare-hare,” in ji Kyaftin Kovangiya.

Kyaftin Kovangiya ya ce wannan nasara na zuwa ne bayan bincike da leƙen asiri da aka gudanar tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro da sauran hukumomin ƙasa.

Ko da yake ana samun ci gaba a fagen yaki da ta’addanci a Arewa maso Gabas, amma har yanzu matsalar tsaro na ci gaba da addabar sassan ƙasar, musamman a jihohin Zamfara, Katsina da wasu yankunan Borno, inda mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da kai hare-hare kan fararen hula da dakarun.

Rahotanni sun nuna cewa, hare-haren ‘yan ta’adda na haifar da ƙalubale ga abinci da zaman lafiyar jama’a, musamman ga manoma da ke fuskantar barazanar kisa ko biyan haraji kafin su iya zuwa gonakinsu.

A wasu yankunan, ’yan bindiga na tilasta wa mutane biyan kuɗin kafin su shiga gona, lamarin da ke hana dubun dubatar fararen hula gudanar da harkokin noma, wanda hakan na ƙara tsananta matsin tattalin arziki da yunwa a yankunan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP Jihar Adamawa jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

A yau Laraba ne aka bude bikin baje koli karo na 22, na Sin da kasashe membobin kungiyar ASEAN ko (CAEXPO), da kuma taron dandalin kasuwanci da juba jari na Sin da ASEAN ko CABIS, a birnin Nanning na jihar Guangxi ta kabilar Zhuang mai cin gashin kai dake kudancin kasar Sin.

A shekarun baya bayan nan, Sin da kungiyar ASEAN, sun ci gaba da cimma manyan nasarori tare a fannin bunkasa dunkulewar tattalin arzikin shiyyarsu, da fadada damar bai daya ta cudanyar mabambantan sassa, a gabar da ake fuskantar yanayin tangal-tangal a duniya.

Wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, ta shaida yadda kaso 92.8 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyi suka amince cewa, baje kolin CAEXPO ya bayyana yadda Sin da kungiyar ASEAN suka himmatu wajen bunkasa bude kofa bisa matsayin koli, da kare tsarin cinikayya cikin ’yanci da kasancewar mabambantan sassa.

Kafar CGTN ta gabatar da kuri’ar ne da harsunan Turanci, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci, da yaren Rasha, inda kuma mutane 6,260 suka bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’ao’i 24. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasha Ta Kai Hare-Hare A Ukraine Cikin Dare
  • Wata mata ta ƙone fuskar ’yar mijinta da tafasasshen man girki a Borno
  • Dakarun Sojin Kasar Yamen Su Kai  Hare-hare A Muhimman Wurare A HKI.
  • Akasarin masu kai mana hare-hare daga jihohin da suka kewaye mu suke – Gwamnatin Filato
  • HKI Ta Kai Hare-Hare Kan Wurare Har 5 A Kudancin Kasar Lebanon
  • Sojoji Sun Raba Takin Zamani Ga Manoma A Katsina
  • Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato
  • Gwamnatin Kano Ta Aika Dalibai 588 Zuwa Jihohin Arewa 13 A Karkashin Shirin Musanya
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi