Aminiya:
2025-08-05@16:34:02 GMT

Buni ya shirya bikin karrama daliban da suka lashe gasar duniya

Published: 5th, August 2025 GMT

Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni, ya shirya da wani gagarumin biki domin karrama Nafisa Abdullah ’yar shekara 17 da Rukayya Muhammad Fema ’yar shekara 15, wadandan ’yan asalin jihar ne, bayan sun lashe gasar duniya da aka gudanar da kasar Birtaniya.

Nafisa ta lashe Gashar Iya Turanci ta Duniya a yayin da Rukayya ta lashe Gasar Muhawar ta duniya, inda suka doke kasashe 69 a Gasar TeenEagle na shekarar 2025 da aka gudanar a birnin Landan.

Bayan doke dalibai sama da 20,000 da suka fafata a gasar inda suka wakilci Najeriya daga Kwalejin Nigerian Tulip (NTIC) da ke Jihar Yobe.

Nafisa da Rukayya dukkansu sun ci gajiyar shirin tallafin karatu na Gwamna Mai Mala Buni wanda ya kunshi cikakken dawainiyar karatun dalibai 890 a NTIC.

Gwamna Buni ya bayyana wannan nasara da ’yan matan suka samu  a matsayin babban abin alfahari ga jiha da kuma Najeriya baki daya.

“Wadannan manyan ayyuka ne da ke sa mu yi alfahari da kuma tabbatar da saka hannun jarin gwamnati a fannin ilimi,” in ji Gwamna Buni.

Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da bayar da tallafin karatu ga kowane yaro a jihar domin samun damar zuwa makaranta, ya kuma yi qira ga iyaye da su ba su haxin kai.

A halin yanzu, akwai kimanin daliban jihar Yobe 40,000 da ke samun tallafin karatu na gwamnati da ke karatun kwasa-kwasai daban-daban a jami’o’i da sauran manyan makarantu a Najeriya da kasashen ketare.

Idan dai ba a manta ba a ’yan watannin da suka gabata jihar ta yi bikin yaye dalibai 167 da suka ci gajiyar shirin tallafin karatu da jihar ta samu wadanda suka kammala karatunsu a fannin likitanci da kwamfuta da kimiyyar injiniyanci daga jami’o’in kasar Indiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gasar duniya Nafiya Rukayya tallafin karatu

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni ya tuhumi sabon Sarkin Gudi, Alhaji Ismaila Ahmed Gadaka da ya jagoranci zaman lafiya, hadin kai, da ci gaban al’ummar masarautar sa, jiha da kasa baki daya. Gwamna Buni ya yi wannan kiran ne a ranar Litinin yayin gabatar da takardar nadin sarauta ga basaraken a hukumance a majalisar masarautar Gudi. Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara  Kwamishinan ilimi mai zurfi, kimiyya da fasaha na jihar, Farfesa Muhammad Bello Kawuwa ne ya mika takardar nadin ga sabon sarkin a madadin gwamnan. Da yake isar da sakon Gwamnan, Farfesa Kawuwa ya bayyana muhimmiyar rawar da masarautar ke takawa wajen bunkasa ci gaban al’umma, magance rikice-rikice da kuma adana kayayyakin tarihi. Ya bukaci sabon sarkin da ya gudanar da wadannan ayyuka cikin adalci, mutunci, da tsoron Allah.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
  • Gwamnatin Tarayya Ta Karrama ‘Yan Wasan Kwallon Kwando Na Mata
  • Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya
  • ’Yar shekara 17 daga Yobe ta lashe Gasar Turanci ta Duniya
  • Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
  • Ƴan matan Najeriya Sun Lashe Gasar Kwallon Kwando Ta Afirka
  • Gwamnan Neja Ya Bada Umarnin Sake Bude Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai.
  • Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi
  • Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?