Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Raba takardun daukar Aiki Ga Sabbin Ma’aikatan Gona Su 1 ,038

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya raba wa sabbin ma’aikatan aikin gona 1,038 da aka dauka aiki takardun su na kama aiki.

 

Bikin, ya gudana ne a gidan gwamnatin Kano.

 

Da yake jawabi yayin bikin gwamnan ya gargade su da su guji cin hanci da rashawa, ya kuma bukace su da su yi wa jihar hidima cikin himma da gaskiya.

 

 

Ya ce matakin ya nuna wani gagarumin ci gaba a kokarin da jihar ke yi na inganta samar da abinci da kuma habaka arzikin iyali.

 

 

Gwamna Yusuf ya bayyana daukar ma’aikata a matsayin cika alkawuran da ya dauka a lokacin yakin neman zabe da kuma wani muhimmin mataki na cimma wadannan manufofin.

 

“Yau rana ce ta sabuwar dama da cika alkawarin da muka dauka a yakin neman zabe, wadannan ayyuka ba wai kawai za su tallafa wajen samar da abinci ba, har ma da samar da kudaden shiga ga dubban iyalan Kano.”

 

Gwamnan ya bayyana cewa, duk da cewa Kano ta riga ta jagoranci kasar nan wajen yawan ma’aikata, amma duk da haka jihar na bukatar karin biyan bukatun noma na zamani.

 

 

“Muna bukatar karin kwararrun ma’aikatan da za su yi wa al’ummominsu hidima, da tallafa wa manomanmu, da kuma taimakawa wajen kawo sauyi a fannin noma.”

 

Gwamna Yusuf ya gargadi sabbin ma’aikatan da su guji cin hanci da rashawa, rashin zuwa aiki, da rashin tausayi, yana mai jaddada cewa daukar ma’aikata ba wata hanya ce ta wawure dukiyar al’umma ba.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
  • Iran tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Tsakanun Kasashen Yankin
  • Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta
  • Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina
  • Gwamna Yusuf Ya Raba takardun daukar Aiki Ga Sabbin Ma’aikatan Gona Su 1 ,038
  • Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
  • Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
  • Jerin gwanon nuna goyon baya ga al’ummar Gaza a Sydney Australia