Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Shirin Sakin Dukkanin Fursunonin Isra’ila Bisa Sharuddan Da Ta Gindaya
Published: 15th, April 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta sanar da sharudan sakin dukkan fursunonin Isra’ila da take tsare da su
Wani jami’in Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya ce: Kungiyar a shirye take ta sako daukacin fursunonin Isra’ila domin tsagaita bude wuta da ficewa daga Gaza, kamar yadda wani rahoto da tashar talabijin ta Alkahira ta fitar.
Jami’in na kungiyar Hamas ya kara da cewa: A ranar litinin din nan ne haramtacciyar kasar Isra’ila ta ci gaba da kawo cikas ga yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma yin watsi da alkawurran da ta dauka, yana mai cewa kungiyar Hamas ta tabbatar wa masu shiga tsakani da “bukatar bayar da lamuni don tilastawa gwamnatin mamayar Isra’ila aiwatar da yarjejeniyar.”
Yana mai bayyana cewa, “Hamas ta yi aiki mai kyau kuma tare da babban sassauci gami da aiki da ra’ayoyin da aka gabatar mata a cikin shawarwarin tsagaita wuta da musayar fursunonin Isra’ila.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
Shugaban kasar Iran Masud pezeshkiyan a wajen taron zaman lafiya na turkmanistan ya bayyana cewa siyasar kasashe masu karfin fada aji a yammacin Asiya ne suka bawa isra’ila wata dama ta musamman ta kai hare-hare gaba gadi, da hakan ya bata damar kai harin soji kan kasashen yankin ciki har da kasar iran ba tare da fuskantar wani sakamako ba.
Har ila yau shugaba peszeshkiyan da yake bayani a wajen taron zaman lafiya a garin Ashgabat na kasar Turkministan ya kara da cewa harin da Isra’ila ta kai wa iran a watan yuni da ya kai ga shahadar mutane da dama da basu san hawa ba balle sauka ya samu kyakkawar tarba ne ma mai makon yin Allah wadai
Yace babu wani mataki na ladabtarwa da aka dauka ga wadda ta kai harin , ta ma samu cikakkiyar goyon bayan siyasa da soji ne daga kasahen masu ikirarin kare hakkin bil adama da kuma samar da zaman lafiya, matukar aka ci gaba da bada irin wannan dama ta musamman to babu wanda zai iya yin Magana kan zaman lafiya ko kuma wani umarni na kasa da kasa.
Daga karshe shugaba pezeshkiyan ya godewa Turkmenistan da ta dauki nauyin shirya wannan taro wanda ya zo dadai da aka cika shekaru 30 da amincewa da zama yar baruwanmu a wannan kasa, kana kuma yayi kiran cewa suna goyon bayan duk wani shiri na karfafa tunani kan zaman lafiya da tsaro da ci gaban dan adam da na dabi’a .
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan December 12, 2025 Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa December 12, 2025 Duniyarmu A Yau: Iran Da Kokarin Juyin Mulkin Amurka A Yakin Kwanaki 12, Wa Ya Sami Nasara? December 12, 2025 Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai December 12, 2025 Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin December 12, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut December 12, 2025 Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba December 12, 2025 Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026 December 12, 2025 Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza December 12, 2025 Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci