Gwamnatin Jihar Kano ta sake jaddada kudurinta na farfado da harkar ilimi ta hanyar gyara makarantun da suka lalace wanda ta gada daga gwamnatin da ta gabata.

Da yake jawabi yayin wata ziyarar duba makarantu a Makarantar Sakandare ta Murtala Muhammad da ke ƙaramar hukumar Tarauni, Kwamishinan Ilimi, Dr.

Ali Haruna Makoda, ya bayyana halin da wasu makarantu ke ciki a matsayin alamar rushewar tsarin ilimi.

Kwamishinan ya nuna damuwa game da yadda ake amfani da harabar makarantu ba bisa ka’ida ba, musamman yadda wasu mazauna yankunan suka mayar da harabar Makarantar Murtala Muhammad wajen zubar da shara.

Ya tabbatar da cewa za a ɗauki matakin gaggawa don dakile lalacewar muhalli da kuma tabbatar da amintaccen wuri don karatu.

Yayin zagayen nasa, Dr. Makoda ya kuma kai ziyara zuwa Makarantar Sakandare ta ‘Yan Mata da ke Guringawa, inda ya duba aikin gine-gine da gyare-gyare da ke gudana.

Ya yaba da jajircewar ɗan kwangilar wajen cika aikin cikin lokaci da kuma bin ƙa’idojin aikin.

Aikin ya haɗa da gine-ginen bene biyu masu ɗakunan karatu huɗu kowanne, bandakunan ɗalibai da na malamai, da ofisoshin malamai, da gina katangar makarantar da kuma rijiyar burtsatse don samun ruwan sha mai tsafta.

Kwamishinan ya kuma kai ziyara zuwa Makarantar Sakandare ta Tukun Tawa, wacce aka gyara a baya ƙarƙashin shirin 484 Ward Project na jihar, wanda ke karkashin jagorancin ƙananan hukumomi. Ya bayyana wannan a matsayin misali na ci gaba daga matakin ƙasa a fannin ilimi.

Ya jaddada cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf yana nan daram da alkawarin da ya ɗauka na samar da ingantaccen ilimi ga kowanne yaro a Jihar Kano.

Idan za a iya tunawa, a baya Gwamnatin Kano ta amince da kashe biliyoyin naira domin sauya fasalin ilimi da inganta gine-ginen makarantu.

 

Khadijah Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Miyetti Allah ta roki Gwamntin Kwara da ta sa baki kan rufe Kasuwar Kara da Shugaban Karamar Hukuma Ya Yi

An bukaci gwamnatin jihar Kwara da ta gaggauta shiga tsakani kan rufe kasuwar Kara da ke yankin Kwara ta Kudu da shugaban karamar hukumar ya yi domin ceto harkokin kasuwanci daga durkushewa.

 

Shugaban kungiyar Miyetti Allah reshen jihar Kwara, Alhaji Shehu Garba ne ya yi wannan roko a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Ilorin.

 

Sanarwar ta ce shirin rufe kasuwannin Kara da ke yankin Kwara ta Kudu da shugaban karamar hukumar ya yi ba tare da sanin sarakunan gargajiya da shugabanni da masu gudanar da aiki ba, bai dace ba.

 

Ya bayyana cewa kafin daukar irin wadannan shawarwarin da shugaban karamar hukumar ya yi ya kamata a yi shawarwari da yawa don tafiyar da wadanda abin ya shafa.

 

A cewarsa da yawa daga cikin ‘yan kasuwar ba su da masaniyar wannan hukunci, kuma suna cikin kasuwannin Kara da kayansu suna gudanar da sana’o’insu.

 

Ta ce rufe kasuwannin Kara a wannan lokaci zai gurgunta harkokin kasuwanci tare da kara fuskantar kalubalen tattalin arziki da ya addabi iyalai a yankin, jihar da ma kasa baki daya.

 

Yana kira da a gaggauta janye sanarwar da aka fada domin tabbatar da gaskiya da adalci.

 

Shugabannin kananan hukumomin Ifelodun, Isin, Irepodun, Offa, Ekiti, Oke-Ero da kuma Oyun dake jihar Kwara ta Kudu sun bayar da umarnin rufe kasuwannin Kara ba tare da bata lokaci ba saboda tabarbarewar tsaro.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Rufe Makarantu 6 Masu Zaman Kansu A Kano Saboda Karin Kudin Makaranta Da Tilasta Iyaye Sayen Littafai
  • Miyetti Allah ta roki Gwamntin Kwara da ta sa baki kan rufe Kasuwar Kara da Shugaban Karamar Hukuma Ya Yi
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Sauya Sunan Ma’aikatar Mata
  • Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
  • An dakatar da shugabannin sakandare 6 a Sakkwato kan zargin cin amanar aiki
  • Hukumar Bunkasa Ilimin Manyan Makarantu Ta Shirya Taro Na Musamman Ga Jami’anta
  • Gwamnatin Gombe ta gyara hanyoyin kiwo domin daƙile rikicin manoma da makiyaya
  • Gwamnatin Kano Ta Aika Dalibai 588 Zuwa Jihohin Arewa 13 A Karkashin Shirin Musanya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba