Gwamnatin Kano Za Ta Farfado Da Makarantu Tare Da Kara Inganta Fannin Ilimi
Published: 6th, August 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta sake jaddada kudurinta na farfado da harkar ilimi ta hanyar gyara makarantun da suka lalace wanda ta gada daga gwamnatin da ta gabata.
Da yake jawabi yayin wata ziyarar duba makarantu a Makarantar Sakandare ta Murtala Muhammad da ke ƙaramar hukumar Tarauni, Kwamishinan Ilimi, Dr.
Kwamishinan ya nuna damuwa game da yadda ake amfani da harabar makarantu ba bisa ka’ida ba, musamman yadda wasu mazauna yankunan suka mayar da harabar Makarantar Murtala Muhammad wajen zubar da shara.
Ya tabbatar da cewa za a ɗauki matakin gaggawa don dakile lalacewar muhalli da kuma tabbatar da amintaccen wuri don karatu.
Yayin zagayen nasa, Dr. Makoda ya kuma kai ziyara zuwa Makarantar Sakandare ta ‘Yan Mata da ke Guringawa, inda ya duba aikin gine-gine da gyare-gyare da ke gudana.
Ya yaba da jajircewar ɗan kwangilar wajen cika aikin cikin lokaci da kuma bin ƙa’idojin aikin.
Aikin ya haɗa da gine-ginen bene biyu masu ɗakunan karatu huɗu kowanne, bandakunan ɗalibai da na malamai, da ofisoshin malamai, da gina katangar makarantar da kuma rijiyar burtsatse don samun ruwan sha mai tsafta.
Kwamishinan ya kuma kai ziyara zuwa Makarantar Sakandare ta Tukun Tawa, wacce aka gyara a baya ƙarƙashin shirin 484 Ward Project na jihar, wanda ke karkashin jagorancin ƙananan hukumomi. Ya bayyana wannan a matsayin misali na ci gaba daga matakin ƙasa a fannin ilimi.
Ya jaddada cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf yana nan daram da alkawarin da ya ɗauka na samar da ingantaccen ilimi ga kowanne yaro a Jihar Kano.
Idan za a iya tunawa, a baya Gwamnatin Kano ta amince da kashe biliyoyin naira domin sauya fasalin ilimi da inganta gine-ginen makarantu.
Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Faɗaɗa masana’antar makamashin nukiliyar Iran don inganta rayuwar mutanen kasar ne, ba don makamai ba
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya gana da manyan jami’ai a masana’antar makamashin nukiliya ta ƙasar a lokacin ziyarar da ya kai Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran (AEOI).
Shugaban Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Masoud Pezeshkian, ya ziyarci AEOI a ranar Asabar da yamma, inda ya gana da wasu manyan jami’ai a masana’antar makamashin nukiliyar.
A yayin taron, Shugaba Pezeshkian ya jaddada cewa: Abin takaici, farfagandar son zuciya ta sanya ra’ayin “Makamashin nukiliya” ya zama daidai da samar da makaman nukiliya. Ya ce, “Samar da bama-bamai na nukiliya ƙaramin ɓangare ne kawai na sakamakon da ba su dace ba da rashin tausayi na wannan fanni. Sauran wannan masana’antar tana da nufin biyan buƙatun ɗan adam na asali. Manufar Iran da nufin kasar na faɗaɗa wannan masana’antar ita ce biyan buƙatun mutane da inganta rayuwar ƙasar ne, ba don samar da makamai ba.”
Shugaban ya kuma jaddada cewa: “Suna ɗaukar amfani da bama-bamai na nukiliya haramun ne, bisa ga fatawar da Babban Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci ya bayar.” Ya ƙara da cewa: “Ilimin yana cikin tunanin masana kimiyyar Iran, kuma rushe gine-gine da masana’antu ba zai hana kasar ci gaba ba. Za ta sake gina cibiyoyin makamashin nukiliyarta da ƙarfi sosai.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran November 2, 2025 Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani November 2, 2025 Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza November 2, 2025 Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci