Aminiya:
2025-09-24@11:12:27 GMT

Ministan tsaron Ghana da wasu sun rasu a hatsarin jirgin sama

Published: 6th, August 2025 GMT

Wasu manyan jami’an gwamnati biyu a Ƙasar Ghana, sun rasu tare da wasu mutum shida a wani hatsarin jirgin sama da ya auku a ranar Laraba.

Hatsarin ya faru ne a yankin Ashanti da ke Kudancin ƙasar.

Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina Manoma sun koka kan rabon takin gwamnati a Sakkwato

Ministan Tsaro, Edward Omane Boamah, da Ministan Muhalli, Ibrahim Murtala Mohammed, na cikin jirgin soja tare da wasu fasinjoji uku da ma’aikatan jirgin guda uku.

Jirgin ya tashi daga birnin Accra, babban birnin Ghana, zuwa garin Obuasi lokacin da aka daina jin ɗuriyarsa.

Rundunar Sojin Ghana ta ce sun daina samun saƙo daga jirgin yayin da yake cikin tafiya.

Julius Debrah, shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasar, ya bayyana a cikin wani saƙon bidiyo cewa wannan hatsarin babban rashin ne ga ƙasar.

Ya kuma ce dukkanin tutocin ƙasar za a yi ƙasa da su har sai an bayar da sanarwa domin girmama wadanda suka rasu.

Sauran waɗanda suka rasu sun haɗa da Alhaji Mohammed Muniru Limuna (muƙaddashin mai kula da harkokin tsaron ƙasar), Samuel Sarpong (mataimakin shugaban jam’iyyar National Democratic Congress), da Samuel Aboagye (tsohon ɗan takarar majalisa).

Sunan ma’aikatan jirgin da suka mutu su ne Squadron Leader Peter Bafemi Anala, Flying Officer Malin Twum-Ampadu, da Sergeant Ernest Addo Mensah.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hatsarin jirgin sama

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike

Aƙalla jami’an tsaro 53 aka kashe a sassa daban-daban na Nijeriya cikin makonni biyu da suka wuce, bisa ga ƙididdigar da muka tattaro daga rahotannin kafofin yaɗa labarai.

Jami’an da abin ya shafa sun haɗa da sojoji da ’yan sanda da jami’an Hukumar Tsaro da Kare Fararen Hula (NSCDC), jami’an shige da fice da na kwastam, da ma jami’an sa-kai da ke taimaka wa jami’an tsaro, ciki har da ’yan sa-kai na JTF da na ƙungiyoyin tsaro na al’umma da gwamnatocin jihohi suka kafa.

Yawancin waɗanda aka kashe, ’yan bindiga ne suka halaka su yayin da suke ƙoƙarin kare al’umma a lokacin hari, yayin da wasu kuma aka kashe su ne a wuraren binciken tsaro da sansanoninsu.

Wannan adadi ya taƙaita ne kan alkulman da muka tattara daga rahotannin kafofin yaɗa labarai, bai haɗa da wasu hare-haren da ba a bayyana su ba ba.

NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu Mahara sun kashe ’yan sanda a shingen bincike a Kogi

Wani bincike da muka gudanar a watan Disambar bara ya nuna cewa, daga watan Janairu 2023 zuwa Oktoba 2024, aƙalla jami’an ’yan sanda 229 aka kashe a faɗin ƙasar nan.

Binciken ya bayyana cewa ’yan bindiga, ’yan ƙungiyar IPOB da ’yan Boko Haram da ’yan fashi da makami da kuma ’yan ƙungiyoyin asiri ne suka kashe jami’an tsaron.

Sabbin hare-haren sun faru ne a jihohin Benue da Kogi, inda aka kashe ’yan sanda bakwai da wasu jami’an tsaro a lokuta daban-daban a ranar Juma’a da kuma jiya Lahadi.

Baya ga waɗanda aka kashe, an kuma sace wasu jami’an tsaro a harin da aka kai a Binuwai.

A ’yan kwanakin nan, Hukumar Tsaro ta DSS ta gurfanar da mutane tara a gaban kotu bisa zargin hannu a kisan gilla da aka yi a jihohin Binuwai da Filato.

An kai su gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, inda kuma aka tuhumi wani da ake zargi da fataucin makamai bisa mallakar bindigogi ƙirar M16 guda bakwai ba bisa ƙa’ida ba.

Cikin waɗanda aka gurfanar har da Haruna Adamu da Muhammad Abdullahi, ’yan asalin Karamar Hukumar Awe a Jihar Nasarawa, da ake tuhuma da laifuka huɗu kan kashe-kashe a Abinsi da Yelewata a Ƙaramar Hukumar Guma ta Jihar Binuwai a ranar 13 ga watan Yuni.

Haka kuma an gurfanar da Terkende Ashuwa da Amos Alede, dukkansu daga Guma, kan zargin kai farmaki don ramuwar gayya da kuma lalata dukiya, wanda ya haddasa salwantar shanu 12 a garin Ukpam.

 

Daga:

Sagir Kano Saleh, Abdullateef Salau, Idowu Isamotu (Abuja), Hope Abah (Makurdi), Tijjani Labaran (Lokoja) & Abubakar Akote (Minna)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Larijani: Iran na kare tsaron kasa da azama
  • Jihar Kogi Na Cikin Fargaba Yayin Da Kogin Neja Da Benuwe Suka Tumfatsa
  • Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh ya rasu yana da shekara 82
  • Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ribas, Fubara Ya Ziyarci Tinubu A Fadar Gwamnati A Abuja
  • Jirgin Ruwan “Umar Mukhtar” Na Agaji Ya Kama Hanyar Zuwa Gaza Daga Kasar Libya
  • An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike
  • Shettima ya tafi New York don halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya
  • Hatsarin mota ya yi ajalin mutum 4, 16 sun jikkata a Yobe
  • Trump Ya Bukaci Afganistan Ta Mayarwa Amurka Sansanin Jiragen Sama Na bagram
  • Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York