Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
Published: 6th, August 2025 GMT
Ya kuma bayyana cewa, tuni aka mika wanda ake zargin ga hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) domin gudanar da bincike tare da daukar matakin da ya dace.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamishina ya yi murabus kan ƙarbar belin dillalin ƙwayoyi a Kano
Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi, ya yi murabus daga muƙaminsa saboda ce-ce-ku-ce da ya biyo bayan karɓar belin wani wanda ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi da ya yi.
Namadi ya yi murabus ne sa’o’i kaɗan bayan da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karɓi rahoton kwamitin bincike da ya kafa kan lamarin.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Namadi ya ce ya yanke shawarar yin murabus ne don “amfanin jama’a gaba daya” da kuma kare gwamnatin a “yaƙin da take yi da sayarwa da shan miyagun kwayoyi.”
Sai dai ya dage kan cewa ba shi da laifi, amma ya yarda cewa ra’ayin jama’a na da muhimmanci, kuma yana da kyau ya kare kimar gwamnatin.
Tuni Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karɓi murabus ɗin tare da yi wa tsohon kwamishinan fatan alheri.
Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya ce Gwamnatin Jihar Kano na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da adalci da yaƙi da laifukan da suka shafi miyagun ƙwayoyi.
Gwamna Abba ya kuma jaddada muhimmancin dukkan jami’an gwamnati su riƙa yin taka-tsantsan da neman izini daga manyan hukumomi kan batutuwa masu mahimmanci na jama’a.